Abu Abdallah Mohammed II Saadi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abu Abdallah Mohammed II Saadi
sultan of Morocco (en) Fassara

1574 (Gregorian) - 1576 (Gregorian)
Abdallah al-Ghalib (en) Fassara - Abu Marwan Abd al-Malik I Saadi (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa 16 century
ƙasa Moroko
Harshen uwa Larabci
Mutuwa Ksar el-Kebir (en) Fassara, 4 ga Augusta, 1578
Ƴan uwa
Mahaifi Abdallah al-Ghalib
Yara
Yare Saadi dynasty (en) Fassara
Karatu
Harsuna Larabci
Sana'a
Sana'a sultan (en) Fassara
Imani
Addini Mabiya Sunnah

Abu Abdallah Mohammed II, Al-Mutawakkil,sau da yawa kawai Abdallah Mohammed (ya mutune a ranar 4 ga watan Agustan shekarar 1578) kuma ya kasance Sarkin Maroko daga shekarar 1574 zuwa shekara ta 1576. Shi ne babban ɗan Abdallah al-Ghalib kuma ya zama Sarkin Musulmi bayan mutuwar mahaifinsa.[ana buƙatar hujja]

Nan da nan bayan ya hau kan gadon sarauta,ya sa aka ƙashe wani ɗan'uwansa kuma aka tsare wani (Mulay en-Naser, gwamnan Tadla).

Kawun Abu Abdallah, Abd al-Malik, wanda,kamar Abdallah al-Ghalib, dan Mohammed ash-Sheikh ne,ya riga ya gudu zuwa Constantinople a daular Usmaniyya a shekarar 1574.[1] Bayan dawowar Ottoman Algeria,Abd al-Malik yayi nasarar shirya rundunarsa, wacce ta kunshi sojojin Ottoman, kuma a shekarar 1576 ya kutsa cikin Maroko ya cinye Fez daga ɗan ɗan'uwansa, a Kame Fez . Yakin farko ya kasance a al-Rukn a cikin ƙasashen Banu waritin, kusa da Fez. A yakin na biyu kusa da Salé (Rabat) a Jandaq al-Rayhan, Abd al-Malik shi ma ya kayar da ɗan ɗan'uwansa. Yaƙi na uku, wanda shi ma Abd al-Malik ya ci nasara, ya gudana a Taroudannt.

Dukansu Abd al-Malik da Abu Abdallah sun mutu bayan shekaru biyu a Yaƙin Alcácer Quibir, a cikin shekarar 1578.A wannan yakin, Abu Abdallah ya yi yakinsa na ƙarshe da kawunsa Abd al-Malik tare da taimakon abokansa na Portugal .

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

Magabata
{{{before}}}
{{{title}}} Magaji
{{{after}}}