Hajiya Amina Isiyaku Kiru

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Hajiya Amina Isiyaku Kiru
Rayuwa
Sana'a

An haifi Hajiya Amina Isiyaku Kiru (MON) a shekarar alif Dubu daya da dari tara da talatin da tara (1939). Ta rike manyan ofisoshi da dama a Ma'aikatar Cigaban jihar Kano a lokacin; Mataimakin Babban Jami'in Gudanarwa, Babban Jami'in Gudanarwa sannan kuma Babban Jami'in Gudanarwa (SEO) a cikin shekarar 1978.[1] An canja ma’aikatar suna zuwa Hukumar da’ar Ma’aikata a ranar 3 ga watan Maris, shekarar alif 1980, kuma ta zama cikakkiyar kwamishina a hukumar.[2]

Asali[gyara sashe | gyara masomin]

Amina ta fara karatunta a cibiyar horar da mata ta Kano (Girls Training Center), sannan ta wuce Women Training Center a shekarun alif dubu daya da dari Tara da arba'in (1940). Amina ta kasance dalibar Banity College, da ke London, UK.

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Kiru ta fara aiki ne a shekarar alif dubu daya da dari Tara da sittin da hudu (1964) a matsayin mai koyarwa ta 3 na dan lokaci kadan sannan ta kai matsayin mataimakiyar babbar'n jami’in gudanarwa a ma’aikatar Kano saboda kwazonta da bin ka’idar ta. Ta zama Babbar Jami'ar Gudanarwa a ma'aikatar a shekarar alif dubu daya da dari Tara da saba'in da takwas (1978). Ayyukanta na kwazo sun sami Karin girma zuwa matsayi na Babban Jami'in Gudanarwa (SEO) a cikin wannan shekarar, wanda ta gudanar na wasu 'yan watanni. An canza ma ma’aikatar suna zuwa Hukumar da’ar Ma’aikata a ranar 3 ga watan Maris, shekarar alif dubu daya da dari Tara da tamanin (1980), a lokacin mulkin Muhammad Abubakar Rimi, aka nada ta Kwamishiniyar Hukumar Ma’aikata. Daga baya aka sake tura ta zuwa Ma’aikatar Lafiya a shekarar alif dubu daya da dari Tara da tamanin da biyu (1982).

Girmamawa[gyara sashe | gyara masomin]

Kiru ta samu kyaututtuka da dama. A shekarar alif dubu daya da dari Tara da Tara (1999), ta samu lambar yabo ta kasa na matsayin memba na Order of Niger (MON). Ta kuma kasance memba a kwamitin da aka sake kafawa na Kamfanin wallafe-wallafe na Truimph Limited. Ta kasance dattijiya a Majalisar Mata ta kasa (NCWS), kuma mamba a kwamitin ba da shawarwari na Hisbah a Kano.

Littafi Mai Tsarki[gyara sashe | gyara masomin]

  • Kabir, Hajara Muhammad. Ci gaban matan Arewa . [Nijeriya]. ISBN 978-978-906-469-4 . Saukewa: OCLC890820657.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Kabir, Hajara Muhammad ([2010-]). Northern women development. [Nigeria]. ISBN 978-978-906-469-4. OCLC 890820657.
  2. "Reminiscences with Hajiya Amina Isyaku Kiru". Daily Trust. 2018-11-11. Retrieved 2022-05-22.