Aisha Najamu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.


Aisha_Abdulrauf_Najmu

Aisha Najamu jaruma ce a masana'antar fim ta Hausa wato kanniwud tana daya daga cikin kyawawan mata a masana'antar, tayi fice ne a shahararren fim mai dogon zango wato Izzar so, jaruma ce data kware a acting, ta Kuma fito a shahararren fim din Nan Mai suna kishiyata.[1]tana fitowa a wakokin soyayya.

Takaitaccen Tarihin ta[gyara sashe | gyara masomin]

Aisha Izzar so(hajiya nafisa) Cikakken sunan ta shine Aisha najamu , an haifeta a ranar 12 ga watan ugusta shekarar 1997,ta tashi tare da iyayenta da Yan uwa a cikin jihar kano, tayi karatun firamare da sakandiri a garin Kano,bayan ta gama SE ta tafi jami'ar Maiduguri ta cigaba da karatun ta, Haifaaffiyar jihar jigawa ce tayi karatun firamare da sakandiri a garin jigawa daganna ta wuce Jami'ar Maiduguri inda ta Karanci kasuwanci,baban su Yana ma yaran sa auren wuri tayi aure inda ta haifi Yara Yan biyu tun tana yarinyar ta, a yanzun haka Bata da aure,[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://www.haskenews.com.ng/2021/06/wacece-aisha-izzar-soaisha-najamu.html?m=1
  2. https://manuniya.com/2022/12/06/cikakken-tarihin-aisha-najamu-izzar-so/