Ibibia Walter

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibibia Walter
Rayuwa
Haihuwa 8 ga Yuli, 1967 (56 shekaru)
Karatu
Makaranta University of Port Harcourt (en) Fassara
Sana'a
Imani
Jam'iyar siyasa Rivers State People's Democratic Party (en) Fassara

Ibibia Opuene Walter (an haife shi 8 ga Yuli 1967) masanin ƙasa ne na Jihar Ribas, ɗan kasuwa kuma ɗan siyasa. Daga 2004 zuwa 2007, ya yi aiki a matsayin Shugaban Karamar Hukumar Okrika. Daga 2013 zuwa 2015, ya yi aiki a matsayin Sakataren Jam’iyyar Demokradiyyar Jama’ar a Jihar Ribas.

Walter shine wanda ya kafa kuma babban mai hannun jari na kamfanin Lowpel da Geowaltek Nigeria Limited. Yanzu haka shi ne Kwamishina a Ma’aikatar Sufuri ta Jihar Ribas.

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Walter a garin Isaka, karamar hukumar Okrika ta jihar Ribas ga Chief Livington da Misis Amisodiki Walter. Ya halarci makarantar Isaka ta jihar tsakanin 1972 da 1978. Ya yi karatunsa na sakandare a Okrika Grammar School da Government Sea School daga 1979 zuwa 1983. Daga nan ya koma makarantar koyon ilimin bai-daya ta jihar Ribas a Fatakwal inda ya yi karatun A-Levels.

Ilimin jami'a na Walter ya fara ne da shiga Jami'ar Fatakwal. Ya kammala digirinsa na BSc a fannin ilimin kasa kuma ya samu shaidar babbar difloma. Daga baya ya sami digiri na biyu a kan injiniyanci da sanin al'ummun ruwa daga wannan jami’ar.

Walter basarake ne na gargajiya kuma shugaban Pelebo-Nworlu War Canoe House of Isaka. Yana da mata da ‘ya’ya mata biyu, Lolia da Sambi.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

http://riversstate.net.ng/government/executive/chief-ibibia-o-walter/ Archived 2017-03-11 at the Wayback Machine

https://riversstate.gov.ng/government/executive/ Archived 2018-07-25 at the Wayback Machine