Kubra Noorzai
![]() | |
---|---|
Rayuwa | |
Haihuwa | Kabul, 1932 |
ƙasa | Afghanistan |
Mutuwa | 1989 |
Karatu | |
Makaranta |
université de Paris (mul) ![]() |
Sana'a | |
Sana'a |
civil servant (en) ![]() |
Kubra Noorzai haihuwa shekarar (1932) mutuwa shekarar( 1986) ta kasance'yar siyasan Afganistan ce. Ita ce mace ta farko da ta zama ministar gwamnati a kasar,[1] tana aiki a matsayin Ministar Kiwon Lafiyar Jama'a tsakanin shekarar alif dari tara da sittin da biyar (1965) zuwa alif dari tara da sittin da tara (1969).
Tarihin rayuwa
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Noorzai a garin Kabul, daya daga cikin yara tara.Ta yi karatu a ( Lycée Malalaï), kafin ta kammala digiri a Kwalejin Kimiyya a Jami'ar Kabul.[2][3]Daga baya Noorzai ta koma Lycée Malalaï, inda ta zama shugabar ta kuma daga baya ta jagoranci tsangayar mata a jami'ar Kabul. [3]A shekarar 1958 ta koma Faransa, inda ta yi karatu a Jami'ar Paris na shekara guda.[2] [3]Ta yi aiki a matsayin mai duba makaranta na makarantun 'yan mata, [4] kuma ta yi aiki a matsayin darekta na Cibiyar Agaji ta Mata a Kabul. [5]Ta kuma zama shugabar kwalejin tattalin arzikin gida.[6]
Daya daga cikin jagororin masu rajin kare hakkin mata a Afganistan, Noorzai na daya daga cikin matan farko da suka daina sanya mayafi a bainar jama'a, bayan Sarauniya Humaira Begum ta ba da misali da fitowa ba tare da nata ba a shekarar (1959).[4]Ta kasance wakiliyar Afghanistan a (UNESCO) da taron Majalisar Mata ta Duniya a Dublin. [2]A cikin shekarar (1964), Sarki Mohammed Zahir Shah ya nada ta a cikin kwamitin ba da shawara wanda ya sake duba daftarin tsarin mulkin a shekarar (1964), [7] wanda ya bai wa mata 'yancin kada kuri'a da tsayawa zabe.Bayan zaben watan Agusta-Satumba a shekarar (1965) Firayim Minista Mohammad Hashim Maiwandwal ya nada ta Ministar Kiwon Lafiyar Jama'a a ranar( 1) ga watan Disamba shekarar (1965),[8] ta zama ministar mata ta farko a Afghanistan.Ta kasance a ofishin har zuwa shekarar (1969).[9]
A matsayin darektar Cibiyar Mata, an zabe ta a Loya Jirga a shekarar (1977) a lokacin mulkin Shugaba Mohammed Daoud Khan.[10]
Ba ta taɓa yin aure ba, ta mutu a gidanta da ke unguwar Kārte Seh a birnin Kabul a shekara ta (1986). [3]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ George Grassmuck, Ludwig W. Adamec & Frances H. Irwin (1969) Afghanistan, Some New Approaches, p319
- ↑ 2.0 2.1 2.2 Lucie Street (1967) The Tent Pegs of Heaven: A Journey Through Afghanistan, p168
- ↑ 3.0 3.1 3.2 3.3 Kubra Nurzai, 1932-1986, 1st Woman Minister of Afghanistan Abarzanan
- ↑ 4.0 4.1 Tamim Ansary (2012) Games without Rules: The Often-Interrupted History of Afghanistan
- ↑ Information Bulletin 1960 - Library of Congress, p627
- ↑ The Kabul Times Annual, Volume 1, p15
- ↑ Sarfraz Khan (2013) Politics of policy and legislation affectin g women in Afghanistan: One step forward two steps back[permanent dead link] Central Asia Journal, Number 73
- ↑ Breaks Barrier Sarasota Herald-Tribune, 2 December 1965
- ↑ Rosemarie Skaine (2010) The Women of Afghanistan Under the Taliban
- ↑ Suad Joseph & Afsāna Naǧmābādī (2003) Encyclopedia of Women and Islamic Cultures: Family, Law and Politics] p788