Maryam Musa Waziri
An haifi Maryam Musa Waziri a ranar 9 ga watan Nuwamba, shekara ta 1992 a Jihar Gombe, jihar da ke arewa maso gabashin Najeriya. Ta girma a jihar Gombe kuma ta yi karatun firamare da sakandare. Jaruma Maryam Waziri ta yi digiri daga Jami'ar Maiduguri (UNIMAID).
Maryam Musa Waziri na daya daga cikin kyawawan jarumai a masana’antar fina -finan Hausa ta Kannywood. An fi saninta da Maryam Waziri. Maryam Waziri tayi Karatun firamare da na sakandare duk a jihar Gombe, inda aka haife ta.
Jaruma Maryam Waziri ta fito a fina -finan Hausa da dama, kuma a halin yanzu rahotonni sun nuna cewa tana daya daga cikin jarumai masu tsada a masana'antar fina-finanai ta Kannywood.
Maryam ta fito a fina -finai sama da 40 tun lokacin da ta samu kanta a matsayin Jaruma, Maryam Waziri ta fito a shirin fim inta na farko a shekarar 2015.[1]
Wasu daga cikin fina-finan ta
[gyara sashe | gyara masomin]Yakin Mata, Yan Zamani, Amina Juna, Muguwar Mace, Yakin Mata, Labarina, da Dan Halak da dai sauran su.
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]Yakin Mata, Yan Zamani, Amina Juna, Muguwar Mace, Yakin Mata, Labarina, da Dan Halak