Musa Bello

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Musa Bello
Rayuwa
Haihuwa 1919
Mutuwa 1975
Sana'a

Musa Bello (An haife shi a shekarar alif 1919 - Ya rasu a shekara ta alif 1975) shi ne Etsu Nupe na 11 a masarautar Nupe ya yi sarauta daga shekarar alif 1967 zuwa rasuwarsa a shekara ta alif 1975 sannan Etsu Nupe Umaru Sanda Ndayako na 12 ya gaje shi.

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

Mahaifinsa, Bello Maliki, shi ne na bakwai Etsu Nupe. Ya yi karatunsa gaba daya a masarautar Bida sannan daga baya ya zama babban hakimin Badeggi a shekara 1965 da Katcha kafin daga nan ya yi aiki a kamfanin kwangila na Kaduna. Ya kasance daga gidan sarautar Masaba a Masarautar Nupe da Bida. Kaka ne ga Etsu Nupe Yahaya Abubakar na 13 a yanzu, kuma kawu ne ga Etsu Nupe Umaru Sanda Ndayako na 12 duk sun zo cikin gidan sarauta daban amma kakansu ɗaya wato Malam Dendo.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

https://allafrica.com/stories/200309100284.html https://www.dailytrust.com.ng/meet-the-royal-ndayakos-of-bida-262995.html Archived 2020-04-28 at the Wayback Machine