Yarjejeniyar Zaɓuɓɓuka zuwa Yarjejeniyar Ƙasa ta Duniya kan Haƙƙin kula da Tattalin Arziki, zamantakewa da al'adun Jama'a yarjejeniya ce ta ƙasa da ƙasa da ke kafa ƙararraki da hanyoyin bincike don Yarjejeniyar ƙasa da ƙasa kan Haƙƙin Tattalin Arzikin Jama'a da Al'adu su .An kafa ta a ƙarƙashin Majalisar Dinkin Duniya kuma ta amince da ita a ranar 10 ga Disamba shekarar 2008, kuma an buɗe ta don sanya hannu a ranar 24 ga Satumba 2009. Tun daga watan Oktoba na shekarar 2018, bayan da aka fara sanya hannu a yarjejeniyar kawo yanzu akwai sa hannun yarjejeniya kusan 45 da jam'iyyun ƙasashe 24. Ta fara aiki a ranar 5 ga Mayu, shekarar 2013. [1]