2022 Ambaliyar Kinshasa

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdeveniment2022 Ambaliyar Kinshasa
Iri aukuwa
Kwanan watan 13 Disamba 2022
Ƙasa Jamhuriyar dimokuradiyya Kwango

Daga ranar 12 zuwa 13 ga watan Disambar 2022,[1] ruwan sama kamar da bakin kwarya ya bar tituna, ababen more rayuwa da kuma unguwanni da dama a ƙarƙashin ruwa ko kuma sun lalace a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo .

Tasiri[gyara sashe | gyara masomin]

Hanyoyi da dama a tsakiyar birnin Kinshasa sun nutse yayin da aka shafe sa'o'i ana sheƙa ruwan sama kamar da bakin ƙwarya tare da rushewar gidaje da dama. [2] A ƙalla mutane 169 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa. [3] Yawancin waɗanda suka mutun dai na faruwa ne sakamakon zaftarewar ƙasa sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya. [2] A ƙalla gidaje 280 ne suka ruguje yayin da wasu sama da 38,000 ambaliyar ruwa ta shafa. [4] Mutane miliyan 12 da suka ƙunshi galibin mutanen birnin ne ambaliyar ruwa ta shafa.[5]

Bayan haka[gyara sashe | gyara masomin]

Gwamnatin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kwango ta sanar da gudanar da zaman makoki na kwanaki uku a ƙasar .[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "DR Congo: Floods and Landslides - Dec 2022". ReliefWeb. 15 December 2022.
  2. 2.0 2.1 2.2 "DR Congo floods leave more than 120 dead in Kinshasa". BBC News. 14 December 2022.
  3. Dorian Geiger (17 December 2022). "At least 169 dead after devastating floods in DR Congo's Kinshasa". Al Jazeera.
  4. "Landslides kill 141 in Congo". Radio Pakistan. 14 December 2022. Archived from the original on 16 December 2022. Retrieved 7 May 2023.
  5. "Floods and landslides kill scores of people in Kinshasa". The Guardian. 14 December 2022.