Anita Mugeni
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa | 1970 (55/56 shekaru) |
| ƙasa | Ruwanda |
| Sana'a | |
| Sana'a | alƙali da lauya |
Anita Mugeni (an haife ta a shekarar 1970) alkaliya ce 'yar kasar Rwanda kuma shugabar kotun shari'a ta gabashin Afirka (EACJ) wacce ta kasance shugabar riko ta kungiyar lauyoyin kasar Rwanda. [1] [2]
Ilimi da aiki
[gyara sashe | gyara masomin]Anita Mugeni ta sami digirinta na farko a fannin shari'a daga Jami'ar Kasa ta Rwanda a shekarar 1996 sannan ta yi digiri na biyu a fannin shari'a daga FUSL-UC Louvain, Belgium a shekarar 2005. Ta fara aikin shari'a a 1998 a matsayin lauya. Ita ce abokiyar kafa ta MRB Attorneys. Ta kasance mamba a Majalisar Dokokin Gabashin Afirka, kuma ta yi aiki a matsayin kwamishiniyar Hukumar Kula da Ayyukan Jama'a da Kwamitin Ba da Shawarwari na Kasa kan Tarayyar Siyasa ta EAC. [1] An nada ta a Kotun daukaka kara ta Gabashin Afirka a shekarar 2021 hakazalika an nada ta a matsayin shugabar kotun a watan Mayun 2023 inda ta maye gurbin alkalin kotun Tanzaniya, Sauda Mjasiri bayan ta yi ritaya daga kotun. [3] [4] [5]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- 1 2 Karuhanga, James (2023-05-31). "Rwanda's Justice Anita Mugeni designated as EACJ Vice President". The New Times (in Turanci). Retrieved 2023-12-08.
- ↑ "8 judges appointed at East African Court". Monitor (in Turanci). 2021-03-04. Retrieved 2023-12-08.
- ↑ "Defender Profile: Rwandan Lawyer Anita Mugeni - International Bridges to Justice". www.ibj.org (in Turanci). 2009-07-15. Retrieved 2023-12-08.
- ↑ "Hon. Lady Justice Anita Mugeni – East Africa International Arbitration Conference 2023" (in Turanci). Retrieved 2023-12-08.[permanent dead link]
- ↑ "MSN". www.msn.com. Retrieved 2023-12-08.