Antoinette Batumubwira

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Antoinette Batumubwira (an haife ta a shekara ta 1956, a Ngozi, Burundi) 'yar siyasar Burundi ce. Ta kasance ministar harkokin wajen Burundi daga shekarun 2005 zuwa 2009. Tana auren tsohon ministan harkokin waje Jean-Marie Ngendahayo.

A karshen shekara ta 2007, an naɗa Batumubwira a matsayin 'yar takarar da zata gaji Alpha Oumar Konaré a matsayin shugabar hukumar Tarayyar Afirka a zaɓen wannan muƙami a farkon shekarar 2008.[1] Gwamnati ta yi kokarin samun goyon bayan wasu ƙasashen Afirka a takararta, kuma ƙasashen Afirka Great Lakes sun yi alkawarin ba ta goyon baya; sai dai daga baya gwamnati ta janye takararta tare da marawa Jean Ping na Gabon baya.[2]

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Jerin sunayen mata na farko da suka rike mukaman siyasa a Afirka

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Jean-Pierre Nkunzimana, "Burundi seeks to join Commonwealth" Archived Nuwamba, 30, 2007 at the Wayback Machine, The New Vision, November 27, 2007.
  2. "Antoinette Batumubwira withdraws her candidacy for the presidency of the African Union", Burundi Réalités, February 1, 2008.