Asibitin Koyarwa na Jami'a (Lusaka, Zambiya)

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Asibitin Koyarwa na Jami'a
Wuri
Ƴantacciyar ƙasaZambiya
Province of Zambia (en) FassaraLusaka Province (en) Fassara
Babban birniLusaka
Coordinates 15°25′55″S 28°18′49″E / 15.43207°S 28.31367°E / -15.43207; 28.31367
Map
History and use
Opening1934
Offical website

Asibitin Koyarwa na Jami'a (UTH) tsohon asibitin birnin Lusaka ne, kuma shine babban asibitin jama'a a Lusakan, a ƙasar Zambia. Shi ne asibiti mafi girma da gadaje 1,655.[1] Asibitin koyarwa ne, don haka, ana amfani da shi don horar da ɗaliban koyan aikin likitanci na gida a ƙasar, ma'aikatan jinya da ma sauran ƙwararrun ma'aikatan kiwon lafiya. UTH ita ce babbar cibiyar horar da likitoci a Zambia don likitoci, ma'aikatan jinya, jami'an asibiti da sauran kwararrun a fannin kiwon lafiya. Asibitin na bayar da kulawa ta farko, da sauran nau'o'in agaji matakai daban-daban.

Tarihin Asibitin Koyarwa na Jami'ar[gyara sashe | gyara masomin]

An gina asibitin a shekara ta 1910 tare da gadaje 15 a lokacin, kuma an yi shi ne don marasa lafiya na Afirka waɗanda mazaje ke kula da su kawai saboda asibitin ba shi da likitoci da ma'aikatan jinya, a wancan lokaci.[2][3] Tare da yanke shawarar matsar da babban birnin ƙasar daga Livingstone zuwa tsakiyar Lusaka, an shirya shirye-shiryen wani babban asibiti don kula da karuwar marasa lafiya. Saboda haka, an fara sabon asibiti a halin yanzu UTH site-(wani ɓangare na asibitin) a cikin 1934 kuma ya zama asibitin horo a wannan shekarar.[4] UTH tana bayar da kulawa ga marasa lafiya da marasa lafiya na kowanne rashin lafiya, kuma cibiyar ce ta masu neman kwararru daga ko'ina cikin ƙasar.[5]

Wuri[gyara sashe | gyara masomin]

Asibitin da ake takaita sunansa da UTH yana a Lusaka, babban birnin ƙasar Zambiya, kusan nisan kilomita 4 daga gabas da tsakiyar birnin.[6][7]

Fitattun likitoci da malamai[gyara sashe | gyara masomin]

  • Christine Kaseba, likitar fiɗa ƙwararriyar likitan mata da mata, tsohuwar uwargidan shugaban ƙasar Zambia (2011-2014)[8]
  • John S. Kachimba, wani mai kula da lafiya kuma mai ba da shawara ga likitan urologist wanda shine babban editan jaridar Medical Journal of Zambia.[9][10]
  • Aaron Mujajati, ƙwararren likita a fannin likitancin ciki.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Mordernisation | The University Teaching Hospital". www.uth.gov.zm. Retrieved 2020-05-25.
  2. "UTH modernisation: From general to specialist – Zambia Daily Mail". www.daily-mail.co.zm. 3 May 2016. Retrieved 2021-05-19.
  3. "Mordernisation | The University Teaching Hospital". www.uth.gov.zm. Retrieved 2022-05-27.
  4. "Mordernisation | The University Teaching Hospital". www.uth.gov.zm. Retrieved 2020-05-25.
  5. University Teaching Hospital Archived 2012-06-26 at the Wayback Machine ZambianDoctors.com
  6. "Health training | ZUKHWA". www.zukhwa.ed.ac.uk (in Turanci). Retrieved 2021-05-19.
  7. "University Teaching Hospital, Lusaka | ZUKHWA". www.zukhwa.ed.ac.uk. Retrieved 2022-05-27.
  8. Zulu, Delphine (2016-08-16). "Zambia: Kaseba in". Times of Zambia (AllAfrica.com). Retrieved 2016-08-21.
  9. "About MJZ". Zambia Medical Association. Archived from the original on 2 February 2017. Retrieved 30 January 2017.
  10. "Chinese hospital heals sore spot in Zambia". the Guardian (in Turanci). 2013-04-29. Retrieved 2022-11-22.