Chikondi Chabvuta

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Chikondi Chabvuta
Rayuwa
Sana'a
Sana'a environmentalist (en) Fassara

Chikondi Chabvuta mai adalcice ta ƙare muhalli kuma mai kare hakkin mata ne daga Malawi.[1] Memba ce ta AWARD.

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Chabvuta wani bangare ne na Shirin Shugabancin Matasan Afirka (YALI) a farkon shekarunta. Moremi Initiative Leadership Empowerment and Development (Milead) ta amince da ita a matsayin matashiyar ‘yar Afirka don ci gaban jagorancin.[2]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Chabvuta ita ce mai ba da shawara ga yankin Kudancin Afirka a CARE International. Kafin wannan ta yi aiki kan adalcin jinsi da sauyin yanayi ga ActionAid da ƙungiyar manoma ta Malawi. Ta yi magana game da adalci na yanayi da batutuwan jinsi ciki har da a taron sauyin yanayi na Majalisar Dinkin Duniya na shekarar 2021 (COP26) a Glasgow,[3] inda ta ba da labarin abubuwan da ta samu na yin aiki da kananan manoma mata a Malawi waɗanda ke fuskantar da yawa matsanancin yanayin yanayi da ke tasiri ga rayuwarsu. Kafin ta je COP26 ta kasance a Zimbabwe tana duba yadda Cyclone Idai ta kashe kusan mutane 1,300. A shekarar 2022 tana ba da rahoto kan ambaliyar ruwa a ƙasarta da ta yi sanadin mutuwar mutane 80 sakamakon guguwar Tropical Ana tare da nuna cewa har yanzu mutane na murmurewa daga Cyclone Idai.[4]

Ita ce mai magana da yawun kan al'amuran yanayi da The Guardian suka tuntubi,[5] the Washington Post da inews.[6]

New Statesman ta ambaci takaicinta a ƙarshen COP26 lokacin da ta gano cewa al'ummar ƙasar suna ƙoƙarin raunana rubutun da aka amince da su na ƙarshe don rage rage sauyin yanayi.[7]

Ta halarci taron haɗa zumunci da yawa, ayyukan jagoranci da shirye-shirye, kuma abokiyar AWARD ce ga Matan Afirka a Bincike da Ci gaban Aikin Noma.[2]

Rayuwa ta sirri[gyara sashe | gyara masomin]

Chabvuta tana zaune ne a Malawi kuma tana da aure da ’ya’ya uku.[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Vetter, David. "Fair COP? The African Women Showing Why Gender Justice Equals Climate Justice". Forbes (in Turanci). Retrieved 2022-10-28.
  2. 2.0 2.1 2.2 Somanje, Caroline (2021-12-11). "Chikondi Chabvuta: Climate Change enthusiast". The Nation Online (in Turanci). Retrieved 2022-10-28.
  3. Climate Action Network International (10 November 2021). "With four days to go at COP 26, civil society raises concerns over weak proposals on the table". Retrieved 28 October 2022.
  4. Gerretsen, Isabelle (2022-02-01). "Storm Ana's devastation in southern Africa highlights need for early warnings". Climate Home News (in Turanci). Retrieved 2022-11-13.
  5. Kaplan, Sarah (28 February 2022). "Humanity has a 'brief and rapidly closing window' to avoid a hotter, deadly future, U.N. climate report says". Retrieved 28 October 2022.
  6. "World's poorest bear brunt of climate crisis: 10 underreported emergencies". the Guardian (in Turanci). 2022-01-14. Retrieved 2022-10-28.
  7. Nuttall, Philippa (2021-11-13). ""We have been cheated again": Why developing nations feel silenced at Cop26". New Statesman (in Turanci). Retrieved 2022-11-10.