Farah Dagogo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Farah Dagogo
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

11 ga Yuni, 2019 -
District: Degema/Bonny
Rayuwa
Haihuwa Port Harcourt, 29 Nuwamba, 1982 (41 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Farah Dagogo (an haife shi 29 ga Nuwamba 1982) ɗan siyasan Najeriya ne. An haifi Hon. Dagogo a Fatakwal. A 2019 an zabe shi a matsayin wakilin mazabar Degema/Bonny na tarayya a jihar Ribas na jam'iyyar People's Democratic Party. Kafin nan ya taba zama dan majalisa a majalisar wakilai ta jihar Ribas.[1]

Fage[gyara sashe | gyara masomin]

Hon. Farah Dagogo yana da digiri na biyu a fannin zamantakewa. Kafin shiga siyasa, ya kasance kwamandan filin MEND. Ya mika makamansa kuma ya karbi afuwar gwamnati a ranar 6 ga Agusta 2009.[2]

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

An zabi Hon. Dagogo a matsayin dan majalisar wakilai ta kasa a Najeriya a babban zaben 2019 kuma an kaddamar da shi a ranar 29 ga Mayu 2019.[3] A baya ya taba zama dan majalisa a majalisar dokokin jihar Ribas mai wakiltar mazabar Degema. A wannan lokacin shi ne shugaban kwamitin majalisar kan harkokin ilimi, inda ya mai da hankali kan bambance-bambancen batutuwan da suka shafi Jami’ar Jihar Ribas da kuma hanyoyin samar da kudade ga tsarin ilimi na jahohi. Ya kuma tabo batutuwan da suka shafi sauyin yanayi da gurbacewar muhalli a yankin Neja Delta.[4]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Southern PDP governors sacrificed Secondus to get 2023 VP position –Dagogo, Rivers Rep". Punch Newspapers (in Turanci). 2021-11-07. Retrieved 2022-02-22.
  2. "Ex-militants among newly elected lawmakers in Rivers Assembly – Premium Times Nigeria". 15 April 2015.
  3. "Rivers Assembly Education Committee okays change of name for RSUST". Archived from the original on 2017-03-09. Retrieved 2022-12-08.
  4. "Nigeria needs proactive Climate Governance Policy to protect..." 25 May 2019. Archived from the original on 25 May 2019. Retrieved 8 December 2022.