Fatima Musa

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Fatima Musa jaruma ce a masana'antar fim ta Hausa wato Kannywood tana daya daga cikin kyawawan mata a masana'antar ta hausa, anfi kiranta da suna macijiya sakamakon fim din macijiya datayi ta fito a matsayin macijiya, shiyasa ake mata lakabi dashi.

Takaitaccen Tarihin ta[gyara sashe | gyara masomin]

Cikakken- sunan ta shine fatima Musa an haife ta a shekarar 1989, yar kabilar gbaygi wacce anan bangaren ake kira da gwari, masoyan ta suna Kiran ta da fati macijiya sakamakon fim din macijiya da tayi, tsohuwar jaruma ce a masana'antar kanniwud tana daya daga cikin kyawawan mata a masana'antar, Haifaaffiyar jihar niger ce garin nufawa, tayi karatun firamare da sakandiri har zuwa Jami,a a can , tana zaune da Yan uwanta da iyayen ta a jihar nija. Bayan ta gama karatu ne ta dawo cikin jihar Kano saboda ta zamo jaruma, tazo a sa,a domin da farawar ta ta shara ta daukaka[1][2]

Finafinai[gyara sashe | gyara masomin]

  • macijiya
  • Ranar juma,a
  • Galaba
  • Da kishiyar gida

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-07-22. Retrieved 2023-07-22.
  2. http://hausafilms.tv/actress/fati_macijiya_musa