Ibrahim IV na Bornu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibrahim IV na Bornu
Rayuwa
ƙasa Najeriya
Sana'a

Ibrahim IV ya kasance ana yi masa take da Sarkin Musulmi na Kanuri na Bornu daga 1820-1846. Yana daya daga cikin shugabannin da suka gabata daga daular Sefawa.

Rarrabewa akan gaba[gyara sashe | gyara masomin]

Mahaifin Ibrahim, kuma tsohon mai mulkin Bornu, ya yi kira ga El-Kanemi, malamin Islama kuma Jarumi, da ya taimaka ma shi ya yaƙi Fulani da shugabansu Goni Mukhtar. Su biyun sun sami damar kawar da Fulani daga galibin Bornu. Ayayin gwagwarmayan El-Kanemi ya yi ƙarfi, kuma ya kasance barazana ga gidan sarauta na Sefawa, wanda Ibrahim da mahaifinsa suka kafa, Dunama Daga baya aka kashe Dunama a wani yunƙurin kashe El-Kanemi. Dan shi, Ibrahim ya gaje shi. El Kanem kuma akayi rashin sa'a ya mutu a shekara ta 1837, dansa Umar ya gaje shi. Shahararrun sarakunan biyu suna son mamaye madafun iko, har suka dinga yake yake a tsakanin Yan Kanemi da Yan Sefawa. Ibrahim yayi shirin kashe Umar ta hanyar kiran dakaru na waje daga Wadai karkashin umarnin Sarkin Musulmi . Koyaya akayi Umar ya gano shirin, kafin lokacin kuma ya kashe Ibrahim kafin ya gudu daga Bornu. Haka,aka ci gaba da kai hari kan daular Sefawa.