Ibrahim ibn Saleh al-Hussaini

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibrahim ibn Saleh al-Hussaini
Grand Mufti (en) Fassara

Rayuwa
Haihuwa Jihar Borno, 1938 (85/86 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Ibrahim ibn Saleh al-Hussaini

Ibrahim ibn Saleh al-Hussaini Ibrahim Ibn Saleh al-Hussaini CON anfi sanin sa da Shaykh Sharif Saleh an haife shi a ranar 12 ga watan Mayun, shekara ta alif ɗari tara da talatin da takwas 1938) Miladiyya, ya kasance ɗan Najeriya ne, malamin addini, mai wa'azi da da'awa kuma mai fassara Alkur'ani. Shi ne babban limamin Gwamnatin Tarayyar Najeriya.[1] Shi ne ya kafa makarantar Kwalejin Annahda ta Kimiyya da Ilimin Addini Islama (wato Annahda college of science and Islamic studies) a shekara ta 1957 kuma a yanzu shi ne shugaban bada fatawa na Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (wato Supreme Council for Fatwa and Islamic Affairs in Nigeria (NSCIA)).[2][3]

Farkon rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Shehu Ibrahim ibn Sale al-Hussaini a ranar 12 ga watan Mayu na shekarar 1938 a garin fadhaa kusa da dikwa a jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya, mahaifinsa Shehu Saleh sannannen malamin addinin Muslunci ne.[4] [5]


Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

al-Hussaini tun yana yaro karami ya fara karatu a gaban mahaifinsa, daya daga cikin sanannun makarantar addinin Musulunci a cikin Borno a wannan lokacin, daga nan ya tafi kasar Saudiyya, Egypt da Pakistan don ci gaba da karatunsa cike da sha'awar hadisai da Kur'ani. Wasu daga cikin malamansa su ne kamar Sheikh al-qadi abani borno, Abubakar al-waziri Borno, Sheikh Adam al-maharusa Borno, Ahmad Abdulfatahi, Sheikh tijjani usman(zangon bare-bari) Sheikh Abubakar Atik, Muhammad al-arabi bin kubbani, Muhammad Al-Hafiz, Mahmoud Khalil al-hussary, Shehu Ibrahim inyass yana daga cikinsu. Al-hussaini ya karanci harshen turanci a ƙasar London.[6][7]


Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Al-hussaini shi ne shugaban majalisar malamai a zauren bada fatawa ta Najeriya, sannan mamba ne a zauren Majalisar dattawa na Musulmai, al-hussaini ya gama karatunsa a daya daga makarantun addini da ke ƙasar Najeriya. Sannan dalibi ne ga manya-manyan malamai da ke wasu ƙasashen duniya, al-hussaini yana gabatar da karatun tafsirin Kur'ani da hadisai da kimiyya a Muslunci.[8] [9]


Matsayi[gyara sashe | gyara masomin]

Ya rike matsayi da yawa amma ga wasu daga cikinsu;

1.Chairman of Financial Regulation Advisory Council of Experts (FRACE) Central Bank ofNigeria

2.Founder and mentor of the Islamic Renaissance Organization 3.Founding Member Association of Muslim Scholars in Africa (Morocco)[6]

4.Adviser to the Federal Government on Islamic Affairs 1992

5.Assistant Secretary-General for African Affairs in the World Islamic People's Leadership 1989

6.Chairman of Assembly of Muslims in Nigeria (AMIN)

7.Member of the Muslim Council of Elders.[8]

8.Founder of Sheikh Shariff Ibrahim Saleh Islamic Center (SHISIC)

Wallafa[gyara sashe | gyara masomin]

Ya wallafa takardu fiye da dari shida(600) sannan ya wallafa rubutu a wajen tarurruka na addinin musulunci sama da dari biyu(200) dukkansu gaba daya da harshen larabci wanda yake dauke da ilimin kimiyya a musulunci, tarihin manzanni, da hikima.[10][11]

Lambar girma[gyara sashe | gyara masomin]

Ya samu lambar girmamawa da takardar karramawa a wurare da yawa, wasu daga cikinsu;

1.Commander of the Order of the Niger (CON), presented to him by the President andCommander-in-Chief of the Armed Forces of the Federal Republic of Nigeria, Abuja, 2008.

2.Doctorate Degree of Science (HNORIS COUSA) Conferred On him, at the 3RD Convocation Ceremony of the Nigerian Turkish Nile University, Abuja, On Saturday, 13TH June 2015.

3.Order of the Republic in Science and Arts Arab Republic of Egypt 1993.

4.Certificate of Merit from the National Union of Students of the State of Borno 1985. 5.Certificate of Merit from the Students Union of the Faculty of Sharia and Law 1995.

6.Certificate of Appreciation from the students of the Faculty of Law, University of Midogray 1995.

7.Certificate of Appreciation from the Ambulance Department of Jama'atu Nasr Al-Islam Group 1996

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Highest ranking Islamic figure, Grand Imam of al-Azhar, visits Nigeria". Retrieved 2019-09-16.
  2. "The muslim 500". Retrieved 2014-09-16.
  3. News, Morocco World (2017-12-09). "King Mohammed VI Defense of Islam Sets 'Modern' Model: African Ulema". Morocco World News. Retrieved 2019-09-18.
  4. https://www.themuslim500.com/profiles/he-sheikh-ibrahim-salih/
  5. https://twitter.com/nileuni/status/609693439517659136
  6. https://www.premiumtimesng.com/news/top-news/190963-%E2%80%8Bbuhari-sultan-saleh-listed-among-worlds-top-50-muslim-leaders.html) . 3 October 2015.
  7. https://aminiya.dailytrust.com.ng/jibi-za-a-kaddamar-da-gidauniyar-cibiyar-sheikh-sharif-saleh/ Archived 2019-09-30 at the Wayback Machine) . Aminiya(in Hausa). Retrieved 2019-09-30.
  8. https://allafrica.com/stories/201301141069.html. "Annahada first aid group of Nigeria
  9. http://www.fatwaacademy.org/viewmember.aspx?ID=46[permanent dead link]) . Retrieved 2019-09-16
  10. https://www.moroccoworldnews.com/2017/12/235929/king-mohammed-vi-islam-modern-model-african-ulema/).MoroccoWorldNews(inHausa).Retrieved2019-09-18[permanent dead link].
  11. https://www.bbc.com/hausa/labarai-54645289).23October2020[permanent dead link].