Ibrahim Khalid Mustapha

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibrahim Khalid Mustapha
Rayuwa
Sana'a

Ibrahim Khalid Mustapha ɗan siyasar Najeriya ne kuma ɗan majalisar dattawa mai wakiltar mazaɓar Kaduna ta Arewa a majalisar dattawan Najeriya ta 10. Ya doke abokin hamayyarsa Sulaiman Abdu Kwari, bayan an zaɓe shi a babban zaɓen Najeriya na shekarar 2023, ɗan jam'iyyar PDP ne.[1][2][3]

Zaɓen Fidda Gwani[gyara sashe | gyara masomin]

Mustapha ya lashe zaɓen fidda gwani na jam'iyyar PDP da ƙuri'u 257, wanda hakan ya bashi damar zama ɗan takarar jam'iyyar PDP a hukumance a babban zaɓen Najeriya na shekarar 2023 da ta gabata.[4] Bayan fafatawa da sukayi da abokin takararsa Sulaiman Abdu Kwari, a ƙarshe kuma yayi Nasara ya lashe zaɓen.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Sahabi, Ahmad (28 February 2023). "#NigeriaDecides2023: PDP wins ALL Kaduna senatorial seats". The Cable. Retrieved 7 December 2023.
  2. "PDP wins Kaduna North Senatorial Seat" (in Turanci). Premiumstimesng.com. 27 February 2023. Retrieved 7 December 2023.
  3. Enyiocha, Chimezie (28 February 2023). "2023 Elections: PDP Clears All Three Kaduna Senatorial Seats". channelstv. Retrieved 7 December 2023.
  4. "Mustapha wins PDP ticket for Kaduna North Senatorial District". premiums times. 24 May 2022. Retrieved 7 December 2023.