Joseph Adefarasin

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Joseph Adefarasin
Rayuwa
Haihuwa Ijebu Ode, 24 ga Afirilu, 1920
ƙasa Najeriya
Mutuwa 28 ga Maris, 1989
Karatu
Makaranta Igbobi College (en) Fassara
Sana'a
Sana'a mai shari'a

Mai girma Justice Joseph Adetunji Adefarasin (an haife shi a shekara ta alif ɗari tara da ashirin da daya 1921 - 28 Maris 1989) ya kasance lauya ne ɗan Najeriya kuma alkalin babbar kotun. Ya kasance ɗaya daga cikin manyan ɗaliban Kwalejin Igbobi, Yaba, Legas daga 1932 zuwa 1939 kuma ya karanci aikin lauya a Jami'ar London daga 1946 zuwa 1949. Joseph Adefarasin shi ne Babban Alkalin Legas na biyu daga 1 ga watan Nuwamba 1974 zuwa 24 ga watan Nuwamban 1985.

Shi ne Shugaban Ƙungiyar Ƙasashen Duniya ta Red Cross da Red Crescent Societies daga 1977 zuwa 1981. Shi ne ɗan Afirka na farko da ya riƙe wannan matsayin kuma an ba shi lambar yabo ta Henry Dunant, wanda shine babbar lambar yabo ta Red Cross ta Duniya.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]