Joseph Kunini

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Joseph Kunini
Rayuwa
Sana'a

Joseph Albasu Kunini, RT. HON (an haife shi 20 ga watan Maris ɗin shekara ta alif ɗari tara da sittin da takwas 1968A.c) ɗan siyasar Najeriya ne wanda a halin yanzu shi ne Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Taraba a Majalisar Ta Tara.[1]

Joseph kunini ɗan jam'iyyar PDP ne wanda yake wakiltar mazaɓar jihar Lau a majalisar dokokin jihar Taraba tun a shekarar 2011.[2]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Joseph Kunini ne a ranar 20 watan Maris ɗin shekarar 1968 a cikin hamshaƙin mai sauƙi kuma talaka amma gidan sarauta na Albasu Kinjoh a Kunini, ƙaramar hukumar Lau ta jihar Taraba. Ya shiga makarantar firamare ta ƙaramar hukumar (LEA) da ke Kunini a cikin shekarar 1979 inda ya samu shaidar kammala karatunsa na farko a cikin shekarar 1985. Daga nan ya samu gurbin shiga makarantar sakandiren gwamnati ta Kunini a cikin shekarar 1985 kuma ya kammala a cikin shekarar 1991. Ya ci gaba zuwa Kwalejin share fage da ke Yola a shekarar 1991 zuwa 1992 sannan ya wuce Jami’ar Jihar Legas sannan ya kammala karatun digiri na farko a fannin Kasuwancin Kimiyya da Digiri na Kimiyyar Masana’antu da Gudanar da Ma’aikata a shekarar 1998 da kuma shekarata 2003, bi da bi.

Ya ci gaba da samun digiri na biyu na Masters of Business Administration (MBA) a Industrial Relations and Strategic Studies daga Jami'ar Jihar Legas da kuma Masters of Science (M.Sc.) a Corporate Governance daga Jami'ar Leeds Beckett a cikin shekarar 2010. Daga baya ya koma Jami'ar Leeds Beckett don yin karatun digirinsa na uku tsakanin shekarar 2012 zuwa 2016 wanda ya ba shi Doctor of Falsafa (PhD) a fannin Kuɗi.[3][4]

Sana'ar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan murabus ɗinsa na son rai a cikin shekarar 2010 daga ma'aikatan gwamnatin tarayya, Kunini ya shiga fagen siyasa, ya tsaya takara kuma ya samu nasara a cikin shekarar 2011 a matsayin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Lau a majalisar dokokin jihar Taraba a ƙarƙashin jam'iyyar PDP. Ya riƙe muƙamin Shugaban Kwamitin Kuɗi da Kasafin Kuɗi na Majalisa tsakanin shekarar 2011 zuwa 2013 kafin a naɗa shi Shugaban Masu Rinjaye tsakanin shekarar 2013 zuwa 2019.

A watan Disambar shekarar 2019 ne aka zaɓe shi a matsayin shugaban majalisar dokokin jihar Taraba bayan murabus ɗin tsohon kakakin majalisar Abel Peter Diah da mataimakin shugaban majalisar Muhammad Gwampo.[5][6] Bonzena Kizito, memba daga Mazaɓar Zing ne ya zaɓi Kunini kuma Ammed Jedua na Mazaɓar Gembu ya mara masa baya. Mambobi 16 daga cikin 24 na majalisar da suka halarci taron sun zaɓi Kunini kakakin majalisar ba tare da hamayya ba.[7][8][9][10]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]