Kay Sifuniso
Appearance
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa |
Mongu (en) |
| ƙasa | Zambiya |
| Karatu | |
| Makaranta |
Chipembi Girls' Secondary School (en) |
| Harsuna | Turanci |
| Sana'a | |
| Sana'a | ɗan jarida |
Kay Sifuniso (an haifeta a shekara ta 1942) yar jarida ce ƴar ƙasar Zambiya, wacce ta shahara a matsayin bakar fata mace ta farko ƴar jaridar Zambia. [1]
Rayuwa
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Kay Sifuniso a Mongu kuma ta yi karatu a makarantar sakandare ta ’yan mata ta Chipembi. A cikin watan Janairu 1964 ta fara aiki a matsayin ƴar jarida a Central African Mail. Bayan watanni 18 ta koma aiki da Jaridar Times of Zambia, inda albashi ta ya ninka. Daga baya ta koma cikin hulɗar jama'a, tana aiki da Tallace-tallace ta Lightfoot, kuma ta yi aiki da Hukumar Kula da Yawon Bude IDO, na tsawon shekara guda. A cikin 1971 ta bar aikin yi na yau da kullun don kula da filin da ita da mijinta suka saya a Lusaka West. [1]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ 1.0 1.1 Kelvin Kachingwe, Kay Sifuniso: First black, female Zambian journalist, Zambia Daily Mail, 21 February 2016.