Lamia Zribi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Lamia Zribi
Minister of Finance (en) Fassara

27 ga Augusta, 2016 - 30 ga Afirilu, 2017
Slim Chaker - Fadhel Abdelkefi (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Majaz al Bab (en) Fassara, 29 ga Yuli, 1961 (62 shekaru)
ƙasa Tunisiya
Karatu
Makaranta Faculty of Law and Political Science, Tunis (en) Fassara
École nationale d'administration (en) Fassara
Tunis University (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Lamia Zribi Yar siyasan Tunusiya ce. Ta yi aiki a matsayin Ministan Kudi har zuwa 1 ga watan Mayun shekara ta 2017, a lokacin da Fadhel Abd Kefi ya gaje ta. An some ta saboda gazawa don hana faduwar kudin dinari na Tunusiya da ci gaba da bunkasa kudaden da ake kashewa a bangaren gwamnati.

Tarihin rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haife shine a shekara ta 1961 a Medjez el-Bab, Lamia Zribi ta fito ne daga lardin Zaghouan. Ta kammala karatun ta ne a tsangayar koyar da shari’a da ilimin siyasa da tattalin arziki na jami’ar ta Tunis, inda ta samu digirin ta na biyu a fannin tattalin arziki a shekara ta 1983 sannan ta shiga makarantar mulki ta kasa, inda ta samu a shekara ta 1993 ta kammala karatun ta na gaba.

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

A shekara ta 2001, ta zama Darakta ne na kashe kudaden waje a Ma’aikatar Raya Kasa da Hadin kai ta Kasa da Kasa, har zuwa shekara ta 2008, ta kasance Darakta ce a Jahar Hasashen.

Ita ce kuma shugabar kamfanin TradeNet (TTN). A ranar 10 ga watan Mayu, 2016, Ministan Kudi ne ya nada ta a matsayin shugabar bankin Kananan da Matsakaita-kudi ta Bankin Kudi ta maye gurbin Souhir Taktak.

A ranar 2 ga watan Fabrairun 2015, an nada ta Sakatariyar Jiha ga Ministan Raya Kasa, Zuba Jari da Hadin Kan Kasa da Kasa a gwamnatin Habib Essid.

A ranar 20 ga watan Agusta, 2016, an nada ta Ministan Kudi a gwamnatin Youssef Chahed. Ita ce mace ta farko da ta fara samun wannan matsayin a Tunisia.

Kora[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 30 ga watan Afrilu, 2017, aka kore ta daga Minista kuma aka maye gurbin ta a kan rikon kwarya da Ministan Raya, Zuba Jari da Hadin Kan Kasa da Kasa, Fadhel Abdelkefi. A ranar 18 ga watan Agusta, aka nada ta shugabar majalisar kididdiga ta kasa da kasa

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]