Luntiang Pilipinas

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Luntiang Pilipinas

Luntiang Pilipinas shiri ne na gandun daji na birni na ƙasa acikin Philippines, wanda Sanata Loren Legarda ya kafa acikin shekara ta 1998, ya himmatu don haɓaka kariyar muhalli da wayar da kan jama'a a tsakanin Filipinas.[1][2]

Shiga zaben 2019[gyara sashe | gyara masomin]

Domin ya tsaya takara a jerin jam’iyyu a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar 2019, Luntiang Pilipinas ya miƙa takardar shaidar tsayawa takara da karɓuwa a ranar 16 ga Oktoba, 2018. Ƙungiyar-jerin jam'iyyar ta zabi Harry Roque, tsohon mai magana da yawun shugaban ƙasa, da Ciara Sotto, mawaƙa da 'yar wsan kwaikwayo. Daga baya, Roque zai janye daga takarar don tsayawa takarar Sanata, kuma Michael Lim Ubac, tsohon ɗan jarida na jaridar Philippine Daily Inquirer, ya maye gurbinsa. Legarda ta kasance ɗaya daga cikin waɗanda aka zaɓa a jerin jam'iyyar, amma ta bayyana aniyarta ta tsayawa takarar majalisar wakilai a Antique.Luntiang Pilipinas ya samu kuri'u 59,096 ne kawai, wanda ya gaza yawan adadin da ake bukata don samun akalla kujera daya a majalisar wakilai.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]