Tekena Tamuno

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Tekena Nitonye Tamuno (28 Janairu 1932-11 Afrilu 2015) ɗan tarihin Najeriya ne kuma mataimakin shugaban jami'ar Ibadan .Ya kasance Shugaban Kwamitin Amintattu na Jami'ar Fasaha ta Bells.

Ilimi da aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Tamuno ya halarci makarantar St Peter's a mahaifarsa ta Okrika don karatun firamare.Bayan ya kammala ya halarci Makarantar Grammar Okrika.Daga 1953 zuwa 1958 ya karanta tarihi a jami'ar Ibadan kafin ya bar kasar a 1960 ya ci gaba da karatunsa a Birkbeck,Jami'ar London da Jami'ar Columbia.A 1962 ya shiga Sashen Tarihi a Jami'ar Ibadan inda ya ci gaba da zama Farfesa Emeritus.

Baya ga aikinsa na gudanarwa da koyarwa, marubuci ne kuma ya jagoranci kwamitocin yi wa gwamnati hidima.

Tamuno ya rasu ne a ranar 11 ga Afrilu, 2015 a Ibadan,yana da shekaru 83.

Jami'ar Ibadan timeline[gyara sashe | gyara masomin]

  • Malami, 1963
  • Babban Malami, 1967
  • Farfesa, 1971
  • Shugaban sashen Tarihi, 1972–1975
  • Dean, Faculty of Arts, 1973-1975
  • Mataimakin Shugaban Jami'a, 1975-1979.

Littattafan da aka zaɓa[gyara sashe | gyara masomin]