Abayomi Sheba
Appearance
1999 - 2003 District: Okitipupa/Irele | |||
| Rayuwa | |||
| ƙasa | Najeriya | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | ɗan siyasa | ||
| Imani | |||
| Jam'iyar siyasa | Peoples Democratic Party | ||
Abayomi Sheba ya kasance ɗan siyasan Najeriya ne wanda aka haife shi a ranar 2 ga watan Mayu 1961 a Ode Irele, ƙaramar hukumar Irele, jihar Ondo, Najeriya. Ya yi karatun Firamare da Sakandare a Ode Irele. Daga nan ya halarci Jami'ar Ilorin, inda ya samu digiri na farko a fannin harkokin gwamnati. Ya ci gaba da karatunsa a Jami'ar Obafemi Awolowo, Ile-Ife, inda ya samu digiri na biyu a fannin harkokin gwamnati daga shekarun 1995 zuwa 1997.[1][2]
Daga shekarar 2007 zuwa 2011, Sheba ya yi karatu a Jami’ar Adekunle Ajasin, inda ya samu digiri na farko a fannin shari’a (LLB) a mataki na biyu, Upper Dibision. Yana da aure da 'ya'ya. Sheba ya yi aiki a matsayin memba na Majalisar Wakilai, da Majalisar Tarayya daga shekarun 1999 zuwa 2003.[3]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Babah, Chinedu (2017-03-20). "SHEBA, Hon. Abayomi". Biographical Legacy and Research Foundation (in Turanci). Retrieved 2024-12-11.
- ↑ Akinbiola, Dr Sunday (2018-09-20). "Breaking!!!!!! Hon. Sheba Abayomi appointed Chairman Federal Character Commission". The Hero Magazine (in Turanci). Retrieved 2024-12-11.
- ↑ "Citizen Science Nigeria". citizensciencenigeria.org (in Turanci). Retrieved 2024-12-11.