Abdessalem Mansour

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abdessalem Mansour
Minister of Agriculture (en) Fassara

29 ga Augusta, 2008 - 17 ga Janairu, 2011
Rayuwa
Haihuwa Sousse (en) Fassara, 19 Nuwamba, 1949 (74 shekaru)
ƙasa French protectorate of Tunisia (en) Fassara
Tunisiya
Karatu
Makaranta Tunis University (en) Fassara
University of Minnesota (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da injiniya

Abdessalem Mansour (an haife shi a ranar 19 ga watan Nuwamban shekarar 1949) ɗan siyasan Tunusiya ne. Ya kasance Ministan Aikin Gona a lokacin tsohon shugaban kasar mai suna Zine El Abidine Ben Ali .

Haihuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Mansour a Sousse, Tunisia . [1] Ya kammala karatunsa a jami’ar Tunis a shekarar 1971, sannan ya samu digiri na biyu a fannin ilimin aikin gona daga jami’ar Minnesota a shekarar 1974.

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Daga shekarar 1974 zuwa 1980, ya yi aiki a Ma’aikatar Noma ta Tunusiya. Ya yi aiki a matsayin mai ba da shawara ga wani kamfanin kasar Kuwaiti daga shekarata 1980 zuwa 1981. [1] Daga 1981 zuwa 1999, ya yi aiki da bankin Stusid . A watan Agustan shekarar 2008, an nada shi a matsayin Ministan Aikin Gona da Albarkatun Ruwa, har sai da aka sauke shi bayan abin da ya biyo bayan zanga-zangar Tunusiya ta 2010-2011 .

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]