Abdullahi Garba Aminchi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abdullahi Garba Aminchi
Rayuwa
Haihuwa 1954 (69/70 shekaru)
Sana'a

Abdullahi Garba Aminchi (an haife shi ranar 11 ga watan Maris, 1954) a karamar hukumar Funtua, Jihar Katsina, Nijeriya. Ya kasance mataimakin gwamnatin gajeran lokaci na NRC karkashin jagorancin Alhaji Saidu Barda daga shekarar 1992 zuwa 1993. Ya kuma kasance mataimakin gwamna na lokacin Alhaji Umaru Musa 'Yar'adua a shekarar 2003.[1][2] Ya kuma rike mukamin jakadan Saudiyya da Oman a lokacin mulkin Umaru Musa Yar’adua bayan ya zamo daga shekarar 2007.[3][4]

Kuruciya da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Abdullahi Garba a ranar 11 ga Maris na shekarar 1954 a karamar hukumar Funtua, Katsina. Ya karanta Engineering daga Kaduna Polytechnic. Daga nan kuma ya samu shaidar kammala karatun digiri a fannin shari'a daga Jami'ar Bayero Kano .[ana buƙatar hujja]

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Abdullahi Garba ya bar fannin injiniyanci ya koma siyasa. Ya fara zama sakataren jam'iyya, sannan Kuma kansila zuwa shugaba sannan daga bisani mataimakin gwamna Saidu Barda a shekarar 1992 sannan a shekarar 2003 zuwa Umaru Musa 'Yar'aduwa.[5] Bayan Gwamna Umaru Musa 'Yar'adua ya tsaya takarar shugaban kasa kuma ya samu nasara a shekarar 2007, Garba ya zama jakadan Najeriya a kasashen Saudiyya da Oman.[1]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 siteadmin (2009-06-29). "How Yar'adua short-changed Southern Katsina". Sahara Reporters. Retrieved 2022-06-16.
  2. Daily, Peoples (2014-11-13). "Garba Aminci joins Katsina guber race under APC". Peoples Daily Newspaper. Retrieved 2022-06-16.
  3. Kperogi, Farooq A. "Yar'adua's Health: Amb. Aminchi's Impossible Grammatical Logic". Notes From Atlanta. Retrieved 2022-06-16.
  4. "BBCHausa.com | Labarai | Yar'adua ya samu sauki matuka". www.bbc.com. Retrieved 2022-06-16.
  5. "Rashin karbar gyara ya sa na fita daga PDP – Garba Aminchi". Aminiya. 2014-10-09. Retrieved 2022-06-16.