Jump to content

Adeyemi Afolahan

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Adeyemi Afolahan
Gwamnan jahar Taraba

28 ga Augusta, 1991 - ga Janairu, 1992
Abubakar Salihu - Jolly Nyame
Rayuwa
Haihuwa Ibadan, 26 Disamba 1949 (76 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Yaren Yarbawa
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Harsuna Turanci
Yarbanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Aikin soja
Fannin soja Nigerian Navy (en) Fassara
Digiri admiral (en) Fassara

Adeyemi Ambrose Afolahan (an haife shi a ranar 26 ga watan Disamba na shekara ta 1949) an naɗa shi mai gudanarwa na farko na Jihar Taraba, a Najeriya a watan Agustan shekara ta 1991 bayan an ƙirƙiro jihar daga wani ɓangare na tsohuwar Jihar Gongola a lokacin mulkin soja na Janar Ibrahim Babangida .Ya miƙa wuya ga zaɓaɓɓen gwamnan farar hula Jolly Nyame a watan Janairun shekarar 1992 a farkon Jamhuriyar Najeriya ta Uku. [1]

An haifi Afolahan a ranar 26 ga watan Disambae shekarar 1949 a Ibadan, Jihar Oyo . Ya yi karatu a Najeriya da ƙasar Ingila. Matsayin da ya riƙe sun haɗa da mataimakin kwamandan, Kwalejin Yaƙin Ƙasa, Abuja, Shugaban Ayyukan Sojan Ruwa da Shugaban Shirye-shiryen Sojan Rukunin.

Da yake magana a wani taro a jihar Legas a watan Mayu na shekara ta 2000, Afolahan ya yi kira ga matasa na Najeriya da su guji yin jima'i ko aƙalla amfani da kwaroron roba don tabbatar da al'umma marar cutar kanjamau.

Shi tsohon jakadan ne a Jamhuriyar Guinea Bissau .

Ya zama Shugaban ƙungiyar Ila Orangun Unity Movement .

  1. "Nigerian States". World Statesmen. Archived from the original on 28 May 2010. Retrieved 2010-05-28.