Ainehi Edoro

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Ainehi Edoro (an haife shi 11 Disamba) marubuciya ce 'yar Najeriya, mai yin suka domin kawo gyara kuma Malamar Jami'a. Ita ce ta kafa kuma ta ke yin wallafaa shafin yanar gizo mai kawo batutuwan da suka shafi adabin Afirka mai suna Brittle Paper. A halin yanzu ita Mataimakiyar Farfesa ce a adabin Baƙar fata na Duniya a Jami'ar Wisconsin-Madison . Bangarorin da ta fi yin bincike a kansa sun haɗa da almara ta ƙarni na 21, adabi a cikin dijital / kafofin watsa labarun yanar gizo, rubutun kirkirarrun labarai masu karade duniya, Adabin Afirka, kirkirarrun labarai na Burtaniya na Zamani, Ka'idojin rubuta kirkirarrun labarai, Falsafar Siyasa, da kuma yin amfani da faharar zamani a wajen bayyanar da halayyar dan'adam.