Aisha Isma'il

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Aisha Isma'il yar siyasa ce a Nigeria wacce ta kasance ministar harkokin mata ta tarayyar Najeriya daga watan yunin shekarar, 1999 zuwa shekara ta, 2003 a cikin majalissar ministocin farko na tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo.[1]

Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Aisha Isma'il ta kammala karatun ta a shekara ta, 1977 a jami'ar Ahmadu bello dake Zaria tare da digirin farko a fannin ilimin zamantakewar dan adam, daga baya ta sami digiri na biyu a fannin tattalin arziki daga kwalejin jami'ar Swansea dake Wales kasar Birtaniya.[2]

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

A shekara ta, 1978 ta fara aikinta a matsayin jami'ar kula da jin dadin jama'a a jihar kano. A shekara ta, 1982 ta shiga ma'aikatar shugabar sashe, bayan shekara guda sai ta koma ma'aikaciyar cigaban jama'a, masata, wasanni da al'adu ta jihar kano inda daga baya aka nada ta shugabar sashin kula da mata da Dangantakar iyali na tattaunawar zamani da maido da tattalin arziki, wani shiri na ne na tattara shugaban kasa na mulkin soja janar Ibrahim Babangida.

A shekarar, 1988 ta zama mace ta farko da ta fara zama babbar daraktan mata da cigaban yara ta jihar kano. A shekarar, 1990 an nada ta ministar gwamnatin jihar kano a matsayin mace ta farko data fara aiki a kwamishina a ma'aikatar cigaban jama'a, masata, wasanni, da al'adu. A shekara ta, 1991 yayin da take aiki a matsayin kwamishina ta shugabanci kwamitin tattaunawa mai cike d cece-kice game da dokar yara da matasa wacce ita ce dokar kananan yara ta jihar kano. A shekarar, 1992 ta zama darekta janar na farko a hukumar mata ta kasa.[3]


Tsakanin shekarar, 1992 da shekara ta, 1994 ta kasance shugabar kwamitin gudanarwa da yankin Africa kan hadakar mata a cigaban hukumar tattalin arzikin majalissar dinkin duniya ta afrika, kuma tayi aiki a matsayin mamba a kungiyar kasashen duniya da dama a shekara ta, 1992 itace shugabar wata wakiliyar africa a madadin majalissar dinkin duniya kan matsayin mata a Vienna, Austria a cikin shekara ta, 1993 ta kasance manzo ta musamman ga kungiyar hadin kan afrika (yanzun tarayyar Afrika) game da kafa shirin mata a Addis Ababa na kasar Habasha ta kuma kasance wakiliya ta musamman a taron asusun tallafawa cigaban aikin gona na duniya (IFAD) kan matan karkara a Brussels Belgium kuma wakiliya a taron IFAD kan mata da cigaban karkara a Geneva na kasar Switzerland a shekara ta, 1994.

A watan yunin shekara ta, 1999 shugaba Oluswgun Obasanjo ya nada ta a matsayin ministan harkokin mata na tarayyar da cigaban matasa. A matsayin ta na minista tayi aiki a kamfaninta na minista tayi aiki a kan manifofin kasa na mata da tsara kuma taba da gudunmuwa wajen zartar da dokar kare hakkin yara a shekara ta, 2003 dokar mai shafi 230 wacce ta tsara hakkin yara a matakin tarayya ya jawo su ka daga jihohin da shari'a ke iko a lokacin da take wayar da kan jama'a game da yaduwar cutar VVF sannan ta ce anan gaba ayyukan tiyata na cutar zu su zama kyauta a duk asibitoticin ta kuma gargadi iyalai game da illolin yin kaciyar mata sannan tayi Allah wadai da auren kananan yara a shekara ta, 2002 tayi maraba da wanke safiya hussaini wata mata da aka yankewa hukuncin kisa karkashin shari'ar musulunci saboda aikata zina a watan oktoba na shekara ta, 2002 a matsayin na memba a jam'iyar adawa ta Alla Nigeria peoples party (ANPP) an matsa mata lamba da ta bar gwamnatin dake karkashin jam'iyar PDP ki barin ta a cire ta daga ofis bayan Olusegun Obasanjo ya lashe zaben shugaban kasa na shekara ta, 2003.

Aje Aiki da Iyali[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan barin aikin jama'a sai ta sadaukar da kanta ga rayuwar sirri daga baya ta halarci taron kasa na shekara ta, 2014 a matsayin wakiliya daga jihar kano itama memba ce ta kungiyar nijar kuma bai karbar kyaututtuka da dama gami da babbar kyauta a cikin Councilungiyar ofungiyar mata ta asa NCWS

Tayi aure kuma tana da yara hudu.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://sunnewsonline.com/ex-minister-aisha-ismail-blasts-inec-says-body-symbol-of-nations-failure/
  2. https://dailytrust.com/celebrating-the-girl-child-ex-minister-challenges-govt-to-bring-back-qualitative-education/
  3. https://sunnewsonline.com/hooligans-idiots-began-politics-of-money-in-nnigeria-hajiya-ismail-ex-minister/