Ambaliyar Sudan ta 1988

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ambaliyar Sudan ta 1988

A farkon watan Agustan shekarar 1988 ne aka yi mummunar ambaliyar ruwa a Khartoum babban birnin ƙasar Sudan .[1] A ranar 4 ga watan Agusta, yankin Khartoum ya sami ruwan sama mai inci 8.4 (210 mm) a cikin sa'o'i 24, fiye da sau biyu na ruwan saman shekara-shekara. [1] An kuma yi ruwan samar kamar da bakin ƙwarya a ranakun 11 da 13 ga watan Agusta [1] Ruwan sama da ambaliyar ruwa da ta biyo baya sun lalata gidaje kimanin guda 127,000 da suka tanadi kusan mutane 750,000 (waɗanda mafi yawancin su sun yi gudun hijira daga wasu wurare a Sudan). [1] Bugu da ƙari, samar da abinci da ruwa, tsaftar muhalli, sufuri, da sadarwa sun lalace sosai. [1] Mutane guda 80 ne suka mutu sakamakon ambaliyar.[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 1.3 1.4 "International Notes Health Assessment of the Population Affected by Flood Conditions -- Khartoum, Sudan". Morbidity and Mortality Weekly Report. US Centers for Disease Control. January 6, 1989. Archived from the original on 2001-02-19. Retrieved 2020-10-15. This article incorporates text from this source, which is in the public domain.
  2. Kramer, Robert S.; Lobban, Richard A. Jr.; Fluehr-Lobban, Carolyn (2013-03-22). Historical Dictionary of the Sudan (in Turanci). Scarecrow Press. pp. xlviii. ISBN 978-0-8108-7940-9.