Damas Ndumbaro

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.


Damas Daniel Ndumbaro (an haife shi a ranar 14 ga watan Yuni 1971) ɗan siyasar Tanzaniya ne, lauya kuma Ministan Shari'a da Tsarin Mulki.

Ya kasance ministan albarkatun ƙasa da yawon buɗe ido kuma ɗan siyasa wanda a halin yanzu ya zama ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Songea Urban na Chama Cha Mapinduzi a karo na biyu tun a shekarar 2015. Har ila yau, shi ne mukaddashin babban jami'in hukumar kula da layin dogo na Tanzaniya-Zambia tun daga watan Maris 2013.[1][2] Ya kasance mai ba da shawara kuma malami a fannin shari'a a Jami'ar Budadden Jami'ar Tanzaniya (Open University Tanzania) kafin shiga harkokin siyasa kuma ya lashe zaɓen kuri'u mafi rinjaye a mazaɓar Songea Urban a karkashin jam'iyyar CCM mai mulki.

Aikin siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin shekarar 2018, Shugaba John Magufuli ya naɗa shi a matsayin mataimakin ministan harkokin waje da hadin gwiwar kasashen gabashin Afirka.[3] A watan Disamba 2020 bayan babban zaben 2020, a majalisar ministocin Magufuli ta 2 an naɗa shi ministan albarkatun ƙasa da yawon buɗe ido.[4] Ya ci gaba da wannan aiki bayan rasuwar Magufuli, duk da haka, a watan Afrilun 2022 an naɗa shi sabon Ministan Tsarin Mulki da Shari’a a majalisar Samia Suluhu.[5] A ranar 1 ga watan Satumba, 2023, biyo bayan sake fasalin majalisar ministocin Samia Suluhu, ya karɓi sabon muƙamin ministar al'adu, fasaha da wasanni.[6]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Change of management at TAZARA". 2 March 2013. Archived from the original on 2 March 2013. Retrieved 2 March 2013.
  2. "Profile:Damas Daniel Ndumbaro". Legal Information Institute. Retrieved 2 March 2013.
  3. "Foreign Ministry Tanzania". Archived from the original on 2017-11-21.
  4. "Analysts scrutinise Magufuli's latest cabinet". The Citizen (in Turanci). Archived from the original on 2020-12-12. Retrieved 2020-12-24.
  5. "Tanzania President Samia makes mini Cabinet reshuffle". The East African (in Turanci). 2022-04-01. Retrieved 2023-03-01.
  6. Admin (2023-09-01). "Tanzania Cabinet Reshuffle: President Samia Announces Key Appointments and Changes". TanzaniaInvest (in Turanci). Retrieved 2023-09-11.