Hadiza Seyni Zarmakoye 'yar siyasa ce 'yar Nijar, wacce aka zaba a matsayin 'yar majalisar dokokin Jamhuriyar Nijar bayan zaben 'yan majalisar dokoki na ranar 27 ga Disamba 2020 a Nijar. Tana daya daga cikin ’yan majalisar mata 50 na wannan majalisa. Tana wakiltar yankin Dosso[1] kuma an zabe ta a cikin jerin jam'iyyar ANDP. Hadiza Seyni ita ce mataimakiyar shugabar majalisar dokoki ta biyu. [2][3][4] A ranar 21 ga Mayu, 2021, an zabe ta a matsayin shugabar karramawar 'yan majalisar mata a Nijar. [5]