Hajiya Zainab Maina

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Hajiya Zainab Maina
Minister of Women Affairs and Social Development (en) Fassara

2011 - 2015
Josephine Anenih - Aisha Alhassan
Rayuwa
Haihuwa 7 ga Augusta, 1948 (75 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Hajiya Zainab Maina, FCIA, MFR (an haife ta ranar 7 ga watan Agusta, 1948) a Jihar Adamawa da ke Arewacin Najeriya. Ta kasance tsohuwar ministan mata da walwalar jama'a ta Gwamnatin Tarayya Najeriya, wadda aka naɗa ta a watan Yulin shekarar 2011.[1][2]

Ilimi da Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Zainab Maina ta fito ne daga jihar Adamawa dake Arewa Maso Gabashin Najeriya. Ta yi karatu a "Kaduna Polytechnic" inda ta samu Diploma a fannin Gudanarwa da kuma karatun gaba da Diploma ND a fannin girke-girke da kula a otel (Catering and Hotel Management). Bugu da ƙari, ta kuma samu shaidar karatun sakataranci (Secretarial Studies) a "Federal Training Centre Kaduna" , sannan kuma a cibiyar "Centre for Development & Population, Washington DC", dake USA inda ta samu karatu a kan "Institution Building Activities" .

Sannan Kuma ta auri Alhaji Umar Joji Maina, Ɗan-Malikin Mubi dake Jihar Adamawa kuma suna da 'ya'ya tare.

Aikin Gwamnati da kuma Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Kafin a ba ta matsayin minista a cikin watan Julin 2011, Maina ta kasance:

  • Board Chairman, National Commission for Nomadic Education, Kaduna (2009–2011);
  • Board Chairman, Garki Microfinance Bank (1998);
  • Board Chairman, NCWS, Garki Microfinance Bank, Abuja (1997);
  • Deputy Chairman, Police Community Relations Committee FCT Command (1998-Date);
  • Member, Vision 2010 Committee (1997);
  • Board Member, National Programme on Immunization (1998–2000);
  • Board Member, Adamawa State Primary Schools Board (1991–1994);
  • Board Member, Family Economic Advancement Programme (FEAP) (1997–2000).

Ta kasance shugabar ƙungiyar National Council for Women Societies (NCWS) na Najeriya. Maina na daga cikin masu fada aji a jam'iyyar PDP mai ci na lokacin sannan ta kasance memba na kwamitin dattawa na PDP, majalisar amintattu na jam'iyyar, da darekta ta musamman a fannin harkokin mata a kamfe na tshohon shugaba Jonathan da mataimakin shi Namadi Sambo (2010), Kwamitin tantance 'yan takara na jam'iyar PDP (2010); Wakiliyar mata ta kasa, Majalisar kamfe na shugaban kasa na jam'iyyar PDP (2007), Wakiliya a taron National Political Reform Conference (NPRC)-2005; Wakiliyar Mata na kwamitin sulhu na jam'iyyar PDP "PDP Reconciliation Committee on theExecutive/Legislative Impasse" (2002); Mai saukan baki na kasa da kasa na taron Home Economics and Consumer Affairs International Council of Women (ICW) da aka yi a Bangkok,Thailand (1993).[2]

Ayyukan da ba na Gwamnati ba[gyara sashe | gyara masomin]

  • Founder/President, Women for Peace Initiative (WOPI) Nigeria
  • Patron, Young Muslim Women Association, Nigeria
  • Sub-Regional Coordinator- Anglophone Africa, International Council for Women
  • Member, World Association of NGOs (WANGO)
  • Member, West African Civil Society Forum (WACSOF)
  • INGO Ambassador, International Non-Governmental Organization(London, UK)

Lambobin Yabo da Karramawa[gyara sashe | gyara masomin]

  • National Award of Excellence towards Women Development Abuja, Nigeria
  • Jean Harris Award – Rotary International
  • Winner of the Distinguished Eagle Achievement Award Newark, New Jersey, USA
  • Amazon Women Award for Contribution towards the Development of Womanhood, Lagos, Nigeria.
  • Africa Youth Congress Award on the authority of the Senate Headquarters, Banjul, the Gambia
  • Merit Award by the Mayor of Atlanta, USA
  • Meritorious Certificate for Loyal and Devoted Services to Development by the Nawar-U-Deen Society of Nigeria
  • Certificate of Recognition – University of Kansas, Lawrence, USA
  • Quintessence Award for Remarkable Contribution to Humanity by media in support of Humanity (MISH)
  • Ambassador for peace by the Universal Peace Federation and the Inter-Religious and International federation for world peace
  • Honorary citizen of Kansas City, USA
  • Fellow, African Business School – FABS
  • Fellow Chartered Institute of Administration – FCIA
  • Member of the Order of the Federal Republic – MFR

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Oduah-Ogiemwonyi is new aviation minister, Maina heads women affairs". The Sun (Nigeria). 4 July 2011. Archived from the original on 8 July 2011. Retrieved 18 July 2011.
  2. 2.0 2.1 "Hajiya Zainab Maina Biography - Age, Family". MyBioHub. 2018-06-04. Retrieved 2022-03-25.