Hassana Muhammad

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Hassana Muhammad (An haife ta ranar 28 ga watan mayu, shekara ta alif 1997).Yar jahar Kaduna ce. Ta kasance shahararriyar yar wasan kwaikwayo ce a cikin masana`antar kannywood.[1] Ta shahara ne a fim din Hauwa kullu.

Farkon rayuwa da karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Hassana ta girma a garin Kaduna. Mahaifinta shine Alhaji Muhammad, sanannen dan kasuwa ne. Ta kammala karatun firamare da sakandare duk a garin Kaduna. daga bisani samu digiri a jami`ar jihar Kaduna[2]

Shahara[gyara sashe | gyara masomin]

Hassana ta samu yin fice ne bayan muhimmiyar rawar da ta taka a cikin fim din Hauwa Kulu wannan fim yasa ta lashe kyautar City People Entertaiment award.

Aikin fim[gyara sashe | gyara masomin]

Ta fara fitowa a fim dintana farko mai suna Mujadala, wand aciki akwai jarumi Umar M. Shareef. Sannan tayi fina-finai da dama ga wasu daga ciki;

  • Mujadala
  • Hauwa Kulu
  • Hafiz
  • Halimatu saadiya
  • Agola. da sauransu..

Iyali[gyara sashe | gyara masomin]

Ta auri ɗan kasuwa kuma mai shirya fina-finai a masana`antar Kannywoood, wato Abubakar Bashir Maishadda

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://ngsup.com/hassana-muhammad-biography-age-career-and-photos/
  2. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2022-04-21. Retrieved 2022-08-02.