Jump to content

Ibrahim Haruna AK

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibrahim Haruna AK

Ibrahim Haruna Abdulkarim wanda aka fi sani da Ibrahim Haruna AK malamin jami'a ne ta Jami'ar Taraya dake Dutsinma. An haifi Ibrahim Haruna AK a watan Nuwamba 28, shekara ta 1988 a garin Katsina dake Arewa Maso yammacin Najeriya.[1]

Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Ibrahim Haruna Abdulkarim yayi karatun firamare da sakandare a makarantun Gwamnati dake jihar Katsina. A shekarar 2010 ne ya kammala Hassan Usman Katsina Polytechnic inda ya karanci Business Administration. Bayan ya kammala a shekarar 2011 ya shiga Jami'ar Umaru Musa Yar'adua inda ya karanci Economics. Ya kammala karatun gaba da Degree wato Masters Degree a Jami'ar Taraya dake Dutsinma.

Aiki da Gogewa[gyara sashe | gyara masomin]

Mal. Ibrahim yayi ayyuka da dama musamman wadanda suka shafi harkar ilimi. Ya fara koyarwa a Makarantar Firamare ta Godiya College Katsina, sannan ya koyar a Makarantar Ilimi ta Amana Community dake cikin Birnin Katsina. Bayan nan kuma yanzu yana koyarwa a Jami'ar Taraya dake Dutsinma.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://scholar.google.com/citations?user=9Tdj1BsAAAAJ&hl=en