Igwegbe Odum
Appearance
| Rayuwa | |
|---|---|
| ƙasa | Najeriya |
| Mutuwa | 1940 |
| Sana'a | |
| Sana'a | ɗan siyasa |
Eze Igwegbe Odum (wani lokaci ana kiransa Cif Igwebe Odum) ɗan siyasar Aro ne ɗan ƙabilar Ibo da aka haifa a garin Mbaukwu na Najeriya a ƙaramar hukumar Awka ta Kudu a jihar Anambra a yau. Igwegbe Odum, ba asalin Aro bane, amma ɗan ƙaura ne kamar yawancin mazauna Arondizuogu. Tare da ƴan uwansa, ya gudu zuwa Arondizuogu a ƙarshen ƙarni na 19. Labarin rayuwarsa ya zama batun Omenuko[1] farkon littafin tarihin Igbo wanda Pita Nwana ya rubuta. Odum ya rasu a shekara ta 1940. Ya kuma kasance suruki ga Ojiako Ezenne na Adazi. Igwegbe Odum bai taɓa komawa ƙasarsa ta Mbaukwu ba. Tare da ƴan uwansa, ya zauna a Ndi-Aniche Uno a Arondizuogu. Zuriyarsu sun haɗa da fitaccen KO Mbadiwe da ɗan uwansa Green Mbadiwe.
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Njoku, Uzochukwu (2005). "Colonial Political Re-Engineering and the Genesis of Modern Corruption in African Public Service: The Issue of the Warrant Chiefs of South Eastern Nigeria as a Case in Point" (PDF). Catholic University of Leuven, Belgium. Archived from the original (pdf) on 2019-07-11. Retrieved 2023-04-15.
Hanyoyin haɗi na waje
[gyara sashe | gyara masomin]- http://www.njas.helsinki.fi/pdf-files/vol14num1/njoku.pdf Archived 2019-07-11 at the Wayback Machine
- http://ahiajoku.igbonet.com/1981/ Archived 2006-06-19 at the Wayback Machine