Malumfashi
|
| ||||
|
| ||||
| Wuri | ||||
| ||||
| Ƴantacciyar ƙasa | Najeriya | |||
| Jihohin Najeriya | Jahar Katsina | |||
| Yawan mutane | ||||
| Faɗi | 158,338 (1991) | |||
| • Yawan mutane | 234.92 mazaunan/km² | |||
| Labarin ƙasa | ||||
| Yawan fili | 674 km² | |||
| Bayanan tarihi | ||||
| Ƙirƙira | 1975 | |||
| Bayanan Tuntuɓa | ||||
| Kasancewa a yanki na lokaci | ||||
Malumfashi (ko Malum Fashi ) ƙaramar hukuma ce a Jihar Katsina, Najeriya. Hedkwatar ta tana cikin garin Malumfashi. Wadda ta Kunshi gundumomi guda 12 wadanda suka hada da Malumfashi A, Malumfashi B, Dayi, Dansarai, Makaurachi,Gangara, Gora, Yammama, Yaba, Marabar Kankara, Marmara,Ruwan Sanyi da Karfi.
Garin Malumfashi garine wanda akasarin mazaunansa Hausawane da Fulani manyan sana'oin mazauna garin sunhadada Noma, Kiwo da Kasuwanci. Manoman garin sunshara wajen noman Masara, Dawa da Auduga.
Sama da kaso 95% nmazauna karamar hukumar Musulmine mabiya Sunna.[1]
Karamar Hukumar Malumfashi tayi iyaka da Karamar hukumar Gwarzo ta jihar Kano daga Gabas maso kudu, Daga Gabas tayi iyaka da Karamar Hukumar Musawa daga Arewa tayi iyaka da Karamar Hukumar Kankara, daga Kudu tayi iyaka da Karamar hukumar Kafur, daga Yamma tayi iyaka da karamar hukumar Bakori.

Tana da fadin kasa kimanin 674 km² da yawan mutum 182,920 a bisa ƙidayar 2006. Shugaban Ƙaramar hukumar na yanzu shine Alhaji Muktar Abdullahi City sannan kuma Mai shari'a Saddiq Abdullahi Mahuta shine Galadiman Katsina kuma Hakimin Malumfashi.
YANAYIN GARIN
[gyara sashe | gyara masomin]Lokacin zafi yana kaiwa kimanin wata 1.9 a malumfashi, wanda yanayin zamin yana kaiwa 95°F sannan yanayin sanyi yana kaiwa kimanin watanni 2.7 wanda kimanin yana kaiwa 86°F a gaba daya shekara yanayi yana caccanzawa.
Lambar ofishin tura sakonni na yankin ita ce 822.[2]
Wakilin majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Malumfashi/Kafur shine Aminu Ibrahim Kafur 2023 to date.
Wakilin amajalissar jiha shine Aminu Ibrahim Saidu 2019 to date.[3]
Malumfashi tana da kyakkyawar mu'amala tsakanin al'ummar kiristoci da Musulmai Hausawa. Suna zaune lafiya da makwabtansu Hausawa da danginsu.
Fitattun mutane
[gyara sashe | gyara masomin]- Late. Justice Mamman Nasir former president Court of Appeal, Kuma Galadiman Katsina daga 1992 zuwa 2019.
- Mai shari’a Saddik Abdullahi Mahuta, wanda ya fi kowa dadewa a kan mulki a jihar Katsina, daga shekara ta alif 1991 zuwa shekara ta 2013 da kuma Galadiman Katsina na 11, Hakimin Malumfashi.
- Senator Bello Mandiya former senator representing Katsina South from 2019 to 2023.
- Sunusi Mamman, Tsohon Vice Chancellor na Umaru Musa Yar'adua University and Sa'in Galadiman Katsina, daga ƙaramar hukumar Malumfashi.
