Mame Birame Mangane (an haife shi ranar 19 ga watan Nuwamban 1969) ƙwararren ɗan ƙwallon ƙafa ne na ƙasar Senegal. Ya buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Senegal wasanni bakwai a 1993 da 1994.[1] An kuma sanya sunan shi a cikin ƴan wasan Senegal da za su taka leda a gasar cin kofin Afrika a shekarar 1994.[2]