Muntaka Connmassie
| |||
| Rayuwa | |||
| Haihuwa | Jihar Kaduna, 10 ga Faburairu, 1946 | ||
| ƙasa | Najeriya | ||
| Mutuwa | 12 Oktoba 2017 | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | mai shari'a | ||
Muntaka Connmassie, CON (10 Fabrairu 1946 - 12 Oktoba Shekara ta 2017) ɗan Najeriya ne masanin shari'a kuma mai shari'a na Kotun Koli ta Najeriya.[1][ Mai shari’a Muntaka Connmassie da farko ya samu horo a matsayin malami, kafin ya shiga aikin lauya; Ya koyar da harshen Larabci da Ingilishi a jihohin Kaduna da Zariya, inda ya yi ritaya daga aikin koyarwa a matsayin shugaban makarantar Larabci ta lardin Fada a jihar Zariya, bayan ya shafe shekaru goma yana wannan sana’a. Ya samu digirin sa na shari’a (LL.B) a shekarar (1976) aka kuma yi masa kiranye, bayan ya halarci makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya da ke Legas a shekarar (1977) Ya kasance lauyan ma’aikatar shari’a ta jihar Kwara (1977 zuwa 1978). da Jihar Kaduna (1978). Tsakanin (1978 zuwa 1988) ya kasance tare da babbar kotu (a Kaduna) a wurare daban-daban; da farko a matsayin mataimakin majistare sannan kuma babban majistare, babban alkalin kotun, mataimakin babban magatakarda, daga karshe kuma ya zama babban magatakarda.[1]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ ^ "As Coomassie, bridge builder, mounts ACF saddle - Arewa". dailyindependentnig.com. Archived from the original on 2016-03-04. Retrieved 1 April 2015.