Reuven Paz

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Reuven Paz
Rayuwa
Haihuwa Haifa (en) Fassara, 14 Nuwamba, 1950
ƙasa Isra'ila
Mutuwa 22 ga Faburairu, 2015
Karatu
Makaranta University of Haifa (en) Fassara
Harsuna Ibrananci
Sana'a
Sana'a Islamicist (en) Fassara da university teacher (en) Fassara
Employers University of Haifa (en) Fassara
Shin Bet (en) Fassara
Reichman University (en) Fassara

Reuven Paz (Nuwamba 14, 1950 - Fabrairu 22, shekarar 2015) kwararre ne na Isra'ila kan Musulunci da ƙungiyoyin Islama a cikin Larabawa da Musulmin duniya, tsirarun Larabawa a Isra'ila, da Tsarin Musulunci.[1] Ya kasance Babban Jami'in Bincike ne a Cibiyar Bincike ta Duniya a Harkokin Ƙasashen Duniya (GLORIA), da Cibiyar Harkokin Kasuwanci (IDC) Herzliya. Ya kuma kasance shugaban bincike a Hukumar Tsaro ta Isra'ila. A can baya, ya yi karatu a Jami'ar Haifa kuma ya yi aiki a matsayin Darakta ne na Ilimi a Cibiyar Harkokin Siyasa ta Duniya don Yaki da Ta'addanci.[2]

An haifi Paz a Haifa ne kuma ya sami Ph.D. daga Jami'ar Haifa a tarihin Gabas ta Tsakiya. Ya buga kasidu goma sha biyu na ilimi kuma ya rubuta littafai hudu kan yunkurin Islama. Bugu da kari, ya ba da shedar kwararru a shari’o’in kotu a Amurka a lokuta da dama.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]