Sani Lulu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Sani Lulu
Rayuwa
Haihuwa 1958 (65/66 shekaru)
Sana'a

Alhaji Sani Lulu Abdullahi (An haife shi ranar 16 ga Afrilun shekarar 1958), tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya ne. Kafin ya zama shugaban NFF a shekarar 2006, ya taɓa zama daraktan wasanni na FCT . Shugabancin na NFF bai daɗe da zama ba saboda hukumar gudanarwar NFF ta tsige shi a shekarar 2010. Shi ne mai gida kuma babban jami'in gudanarwa na makarantar Fosla Football Academy da ke Karshi a babban birnin tarayya .

Tarihin Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Sani Lulu a garin Zariya, jihar Kaduna a ranar 16 ga watan Afrilu shekarar 1958. Ya halarci Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Warri, Jihar Delta daga shekarar 1971 zuwa ta 1976. Bayan ya kammala karatunsa na IJMB a Makarantar Koyon Ilimi ta Zariya a shekarar 1977, ya samu digiri na farko a fannin Quantity Survey daga Jami’ar Ahmadu Bello Zariya a shekarar 1980.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]