Abdelkrim Ghallab
|
| |
| Rayuwa | |
| Haihuwa | Fas, 31 Disamba 1919 |
| ƙasa | Moroko |
| Mutuwa |
El Jadida (en) |
| Karatu | |
| Makaranta |
Jami'ar Alkahira Jami'ar al-Karaouine |
| Harsuna | Larabci |
| Sana'a | |
| Sana'a | ɗan jarida da marubuci |
| Mamba |
Academy of the Kingdom of Morocco (en) |
| Imani | |
| Jam'iyar siyasa |
Istiqlal Party (en) |

Abdelkrim Ghallab (31 ga Disamba, 1919 - 14 ga Agusta, 2017) ɗan jaridar Maroko ne ɗan siyasa, mai sharhi kan al'adu, kuma marubuci. An haifeshi a Fes, Morocco. Ya kasance muhimmin mutum a fagen adabi da siyasa. Yayi karatunsa duka a Jami'ar Al-Karaouine da ke Fez da kuma ta Alkahira .
Ghallab shi ne marubucin littattafai biyar da tarin gajerun labarai. Babban sanannen labarinsa shine Dafann al-m'd (Wanda aka binne a baya), 1966. A cewar Simon Gikandi salon sa na larabci an san shi da "kyakkyawa kuma a wasu lokutan ilimin gargajiya". [1]
A cikin 2000, Haɗaɗɗiyar marubutan Larabawa a Misira sun haɗa da littafinsa mai suna Al-Mu`alîm `Ali (Master Alí) daga cikin ingantattun litattafan Larabci guda 100 a tarihi. A cikin 2001, sashen Al'adu na Maroko ya buga cikakken aikin Ghallab cikin mujalladai biyar. A cikin 2004 an ba shi lambar yabo ta Maghreb na Tunis . An fassara aikinsa a cikin harsuna da yawa. [2]

Ghallab ya mutu a El Jadida a ranar 14 ga Agusta, 2017, yana da shekara 97. [3]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Simon Gikandi, Encyclopedia of African literature, p. 283
- ↑ Salim Jay, Dictionnaire des écrivains marocains, Casablanca: Eddif, 2005, p. 191
- ↑ "Le journaliste et écrivain marocain Abdelkrim Ghallab est décédé" Archived 2017-11-09 at the Wayback Machine In: huffpostmaghreb.com, Retrieved 14 August 2017]