Babban Alkalin Jihar Lagos

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

 

Babban Alkalin Jihar Lagos
position (en) Fassara
Bayanai
Ƙaramin ɓangare na attorney general (en) Fassara
Farawa 27 Mayu 1967

Babban Alkalin jihar Legas wanda aka fi sani da kwamishinan shari'a na jihar Legas shine shugaban ma'aikatar shari'a ta jihar Legas.[1][2] Aikin jami'in shi ne tabbatar da cewa "dokokin jihar sun kasance daidai kuma ana aiwatar da su yadda ya kamata".[3] Babban Lauyan gwamnati yana gudanar da ayyukansa ta hannun ma'aikatar shari'a.[4] Ana nada Babban Lauyan Gwamnati ne na tsawon shekaru hudu, tare da damar zarcewa na wa'adi biyu, da Gwamna ya mika har zuwa amincewar Majalisar Dokoki ta Jiha.[5][6] Moyosore Onigbanjo babban lauyan gwamnati mai ci, wanda Mosediq Adeniji Kazeem ya gabace shi .

Ayyukan doka[gyara sashe | gyara masomin]

A sashe na 195 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999. "Akwai babban lauya a kowace jiha wanda zai zama babban jami'in shari'a na jihar kuma kwamishinan shari'a na gwamnatin jihar bisa ga tanadin da ke sama".[7] Har ila yau, Babban Lauyan yana matsayin Shugaban Fannin Shari'a, wanda ke da alhakin samar da hidimomin shari'a da goyon baya ga jami'an tsaro na gida a cikin jihar kuma yana aiki a matsayin babban lauya a cikin shari'ar jihar.[8] Bugu da kari, Babban Lauyan Gwamnati na Kula da Hukumomin tabbatar da doka.[9][10][11]

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

An kafa ofishin ne a shekarar 1968, shekara guda da kafa jihar Legas. Tun daga kafa ofishin, jami’ai goma sha shida ne suka yi aiki a wannan matsayi, ciki har da Farfesa Yemi Osinbajo, mataimakin shugaban Tarayyar Najeriya a yanzu.[11][12][13][14]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Lagos Rejects Court Decision on Environmental Sanitation, Articles - THISDAY LIVE". thisdaylive.com. Archived from the original on 5 July 2015. Retrieved 24 April 2015.
  2. "Sanitation: Movement restriction still in force, says Lagos". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 6 July 2015. Retrieved 24 April 2015.
  3. "Lagos Attorney General Defends Ban on Hijabs in Schools, Articles - THISDAY LIVE". thisdaylive.com. Archived from the original on 11 November 2014. Retrieved 24 April 2015.
  4. "Court Dismisses 'Deportation' Case against Lagos State, Articles - THISDAY LIVE". thisdaylive.com. Archived from the original on 20 March 2015. Retrieved 24 April 2015.
  5. "Fashola Swears in Atilade as Lagos Chief Judge, Articles - THISDAY LIVE". thisdaylive.com. Archived from the original on 2 April 2015. Retrieved 24 April 2015.
  6. "Sanitation movement restriction still in force –Lagos". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 24 April 2015. Retrieved 24 April 2015.
  7. "Lagos State Government". 23 April 2015. Archived from the original on 2015-03-31.
  8. "Court bars Lagos from privatising probate". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 22 April 2015. Retrieved 24 April 2015.
  9. "Judiciary Workers Suspend Strike in Lagos, Articles - THISDAY LIVE". thisdaylive.com. Archived from the original on 29 June 2015. Retrieved 24 April 2015.
  10. "Review of Lagos State Criminal Law, inevitable - AG - Vanguard News". Vanguard News. Retrieved 24 April 2015.
  11. 11.0 11.1 "How a Pentecostal law professor has helped reshape Nigerian politics". Washington Post. Retrieved 24 April 2015.
  12. "Meet Buhari's running mate, Prof Yemi Osinbajo - Vanguard News". Vanguard News. Retrieved 24 April 2015.
  13. "Finally, Buhari settles for Tinubu ally, Yemi Osinbajo, as running mate - Premium Times Nigeria". Premium Times Nigeria. Retrieved 24 April2015.
  14. Mwalimu, Charles (2005). The Nigerian Legal System. ISBN 9780820471266. Retrieved 24 April 2015.

Template:Lagos State