Bashir Aliyu Umar

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Dr. Bashir Aliyu Umar

Farkon rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Bashir Aliyu Umar an haife shi a cikin garin kano dake a arewancin nageriya da ne ga Mai girma Dan Amar din kano

Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

BAshir yayi karatu a Jami'ar Ahmadu Bello dake cikin birnin Zazzau inda ya karanci Injiniyanci Lantarki, Sannan ya tafi Jami'ar Musuluncci ta Madina, dake kasar Saudi Arabia in ya sami Digirinsa na farko B.A, dana biyu M.A dana Ukku Phd. dukansu a bangaren HAdisi da Kimiyar Addinin Musulunci, Yayi karatun addinin musulunci na Fiqhu,Qur'ani, Tuhidi da Sauran fannonin Addinin Islama a Nageriya da Madina.[1]

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Ya kasance malami a jami'ar BAyero dake Kano, wanda daga baya gwamnatin kano ta gayyace shi domin zama Sakatare na Din-din-din a ma'aikatar Shari'ah ta jahar kano. Aikin shi a ma'aikatar ya kunshi baiwa Gwamna shawara a kan harkokin shari'ar musulunci da kula da tsare tsare da shirye shirye na ma'aikatar.[2] Ya kasance mamba a Commitee na harkar tattalin arziki na musulunci na sabon bankin musulunci da aka bude a wancan lokacin a nageriya mai suna JA'iz Bank, a wannan hali ne ya gabatar da laccoci da mukallu akan harkar bankuna bisa tsari da turbar Musulunci a najeriya, Sannan yayi aiki a matsayin Shugaba na Mashawarta na Addinin musulunci na Bankin Stanbic IBTC Najeriya, kuma yanzu haka mamba ne na Shari'ah Commitee of the International Islamic Liquidity Management Corporation, [3]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]