Fidelis Okoro

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Fidelis Okoro
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

3 ga Yuni, 2003 - 5 ga Yuni, 2007 - Ayogu Eze
District: Enugu North
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

29 Mayu 1999 - 29 Mayu 2007 - Ayogu Eze
District: Enugu North
Rayuwa
Haihuwa Jihar Enugu
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party
Alliance for Democracy (en) Fassara

Fidelis C. Okoro ɗan siyasar Najeriya ne wanda kuma ya kasance Sanata mai wakiltar Enugu ta Arewa Sanatan jihar Enugu a farkon jamhuriya ta huɗu ta Najeriya, wanda ya yi takara a jam'iyyar Alliance for Democracy (AD). Ya kuma fara aiki a ranar 29 ga watan Mayun shekarar 1999.[1]

Bayan ya hau kan kujerar sa a majalisar dattawa a watan Yunin shekarata 1999, Okoro ya zama kwamitocin kula da ayyukan majalisar dattawa, masana’antu (shugaban ƙasa), harkokin ƴan sanda, noma da kuma Neja Delta.[2] Ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar People's Democratic Party (PDP) kuma ya zama abokin Gwamna Chimaroke Nnamani.[3] A cikin watan Disambar 2001, Cif Mike Ejinima, mai neman zama gwamna, ya shigar da ƙarar sa a gaban kotu tare da Nnamani, Ike Ekweremadu da David Atigwe, ɗan majalisar dokokin jihar Enugu.[4] An sake zaɓen shi a cikin watan Afrilun 2003 akan tikitin PDP.[5]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]