Hadiza Muhammad

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Hajiya Hadiza Muhammad wacce aka fi sani da Hadizan Saima fitacciyar jaruma a masana'antar shirya fina-finan Hausa wato Kannywood

Hajiya Hadiza Muhammad wacce aka fi sani da Hadiza Saima. Hadiza fitacciyar jaruma ce a masana'antar shirya fina-finai na Hausa (wato Kannywood). Tana taka rawa sosai cikin fina-finai a matsayin Mahaifiya.[1][2]

Farkon Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Hajiya Hadiza Muhammad a Unguwar Fage dake jihar Kano yar Fulani inda daga bisani ta koma rayuwa a Unguwar Birged dake cikin birnin na Kano. Ta yi karatun firamare a makarantar Gogoro Special Primary School, ta kuma yi sakandire bayan nan sai ta yi aure ta haifi yara guda biyu mace da namiji.[3][4]

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Hajiya Hadiza ta fara sana'ar fim a shekarar 2010 a masana'antar shirya fina-finan Hausa (wato Kannywood) ta daukaka sosai a masana'antar kasancewarta hazikar jaruma mai masoya inda ake mata lakabi da bakya tsufa.

Jerin Fina-finai[gyara sashe | gyara masomin]

Ta fito a cikin fina-finai da dama kamar su:

  • Buburwar Zuciya
  • Dan Marayan Zaki
  • Hajjaju
  • Ummi
  • Kalan dangi
  • Labarina
  • Alaqa
  • A kashe da na da sauran su.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2022-10-12. Retrieved 2022-10-12.
  2. https://jackatapinch.com/hadiza-muhammad-saima-biography-net-worth-age/ Archived 2022-10-12 at the Wayback Machine
  3. https://instagram.com/hadizansaima
  4. http://hausafilms.tv/actress/hadiza_moh_d