Henriette Ekwe Ebongo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Henriette Ekwe Ebongo
Rayuwa
Haihuwa Ambam (en) Fassara, 25 Disamba 1949 (74 shekaru)
ƙasa Kameru
Karatu
Makaranta University of Havana (en) Fassara
Harsuna Faransanci
Turanci
Sana'a
Sana'a ɗan jarida
Kyaututtuka

Henriette Ekwe Ebongo (25 ga watan Disambar shekarar 1949) [1] 'yar jarida ce 'yar kasar Kamaru, mawallafiya kuma 'yar gwagwarmayar siyasa. An ba ta lambar yabo ta Mata masu ƙarfin zuciya a cikin shekarar 2011. [2] [3]

Ebongo tana ba da shawarar 'yancin 'yan jarida, daidaiton jinsi, 'yancin ɗan adam, da shugabanci nagari. Ta kasance mai fafutuka a gwagwarmayar yaki da mulkin kama-karya a shekarun 1980, da yakin da ake yi a halin yanzu na yaki da cin hanci da rashawa na gwamnati, wariyar jinsi da take hakkin dan Adam. A wannan lokacin ta sha fama da danniya da azabtarwa da kuma kai ta kotun soji. [2] [4]

Ita ce mawallafiyar jaridar Babela mai zaman kanta ta mako-mako kuma ta kafa kungiyar Transparency International reshen Kamaru, kungiyar da ba ta gwamnati ba.[5]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Cameroun: Henriette Ebongo Ekwe, mourir plutôt que de trahir". Journal du Cameroun. 14 April 2011. Retrieved 12 July 2018.
  2. 2.0 2.1 "Ekwe Ebongo of Cameroon and nine others win International Women of Courage award". afripol.org. 14 March 2011. Archived from the original on 4 May 2019. Retrieved June 30, 2011.
  3. "Secretary Clinton To Host the 2011 International Women of Courage Awards". 2011-06-30. Retrieved 2017-03-09.
  4. "Embassy Transcripts | Embassy of the United States Bishkek, Kyrgyz Republic". bishkek.usembassy.gov. 8 March 2011. Archived from the original on 6 October 2011. Retrieved June 30, 2011.
  5. "Cameroonian Journo Wins International Women Of Courage Award". news.cameroon-today.com. Archived from the original on May 4, 2019. Retrieved June 30, 2011.