Ibrahim Abdullahi Ɗanbaba

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibrahim Abdullahi Ɗanbaba
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

11 ga Yuni, 2019 -
District: Sokoto South
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

2019 -
District: Sokoto South
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

9 ga Yuni, 2015 - 9 ga Yuni, 2019
District: Sokoto South
Rayuwa
Haihuwa Sabon Birni, 1 ga Janairu, 1953 (71 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Jami'ar Usmanu Danfodiyo
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Ibrahim Abdullahi Ɗanbaba (an kuma haife shi a ranar 1 ga Janairun shekarar 1960) ɗan siyasar Najeriya ne kuma akawu, shi ne Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu Sanatan Jihar Sakkwato a Majalisar Tarayya ta Tara.[1][2]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Ɗanbaba a Sabon Birni, Jihar Sakkwato, ya halarci Makarantar Sakandare ta Gwamnati Gusan inda ya samu shaidar kammala karatunsa na Makarantar Yammacin Afirka (WAEC) a shekarar 1979. Ya wuce Kwalejin Horar da Malamai ta Sakkwato inda aka ba shi NCE a shekarar 1976. Ya karanta Management a University of Sokoto, kuma ya kamala a shekarar 1981. Ya samu digiri na farko a fannin Accounting a Loton College of Higher Education, United Kingdom a 1989.[3]

Sana'ar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Ɗanbaba ya kasance mataimakin gwamnan jihar Sokoto daga shekarar 1999 zuwa 2003.[4] An zaɓe shi a matsayin Sanata mai wakiltar Sokoto ta kudu a watan Maris 2015.[5] A watan Yuni 2018, ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar People's Democratic Party.[6] A ranar 23 ga Fabrairu, 2019 aka zaɓi Shehu Tambuwal a matsayin Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu inda kuma ya samu ƙuri’u 134,204 yayin da Ɗanbaba ya samu ƙuri’u 112,546.[7] A watan Nuwamba, 2019, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Sokoto ta mayar da Sanata Ibrahim Ɗanbaba a matsayin Sanata a Majalisar Dokoki ta ƙasa yayin da aka tsige Sanata Shehu Tambuwal daga muƙaminsa sakamakon soke hukuncin da kotun sauraren ƙararrakin zaɓe ta yi.[8][9][10][11]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]