Jump to content

Ireti Kingibe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ireti Kingibe
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

13 ga Yuni, 2023 -
District: Abuja
Rayuwa
Haihuwa jihar Kano, 2 ga Yuni, 1954 (71 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƴan uwa
Abokiyar zama Baba Gana Kingibe
Ƴan uwa
Karatu
Makaranta Queen's College, Lagos
University of Minnesota (mul) Fassara
Harsuna Turanci
Yarbanci
Hausa
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da civil engineer (en) Fassara
Imani
Addini Musulunci
Jam'iyar siyasa Partij van de Arbeid (mul) Fassara

Ireti Heebah Kingibe (an haife ta 2 Yuni 1954) ta kasance injiniyan gine-gine kuma yar siyasa a Najeriya. An zaɓe ta a majalisar dattawa mai wakiltar Babban Birnin Tarayyar Najeriya (FCT) a zaben Najeriya na 2023 a karkashin Jam’iyyar Labour (LP). Kanwa ce ga Ajoke Mohammed, matar tsohon shugaban mulkin sojan Najeriya Murtala Mohammed.

Ireti Kingibe

Rayuwarta da Ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

Kingibe ta fara karatu a makarantar Emotan preparatory, bayan ta halarci makarantar Queen's College Lagos da Washington Irving High School don karatun sakandare. Ta yi digiri a Civil engineering a University of Minnesota.

Kingibe ta fara aikinta a matsayin Injiniya mai kula da inganci tare da kamfanin Bradley Precast Concrete Inc. daga shekara ta 1978 zuwa 1979. Daga nan sai ta ci gaba da aiki tare da sashin Ma'aikatar Sufuri ta Minnesota, inda ta kuma yi aiki a matsayin injiniya daga shekara ta 1979 da 1991. Ta koma Najeriya don shekara guda ta aiki tsakanin 1981 da 1982. An tura ta aiki a matsayin mai kula da aikin tare da sansanin Sojojin Sama na Najeriya a Ikeja, Legas . [1]

  1. "Ireti Kingibe: Biography, Education, Professional and Political Career, Marriage, Net Worth, and Controversy". NewsWireNGR (in Turanci). 2023-02-22. Retrieved 2023-02-28."Ireti Kingibe: Biography, Education, Professional and Political Career, Marriage, Net Worth, and Controversy". NewsWireNGR. 22 February 2023. Retrieved 28 February 2023.